Al’umma da dama ne suka jima suna amfani da man zaitun a ƙasashe ko yankunan da suke kewaye da kogin Mediterranean, a abinci da kuma wasu cututtuka da ke addabar jikinsu. Bincike da ake gudanarwa yanzu ya taimaka wajen bankaɗo wasu daga cikin ababe masu muhimmanci da ke ƙunshe cikin man zaitun ɗin waɗanda suka sanya […]
Bismillahir Rahmanir Rahim Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai. Tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabi Muhammad, da alayensa da sahabbansa baki daya. Bayan haka, lalle rayuwar dan adam bata tafiya daidai ba tare da hakuri ba; yana bukatar hakuri don inganta addininsa da rayuwarsa, saboda duk wani aiki dole ya hadu da […]
Ita kalmar physics ta samo asali ne daga kalmar “physis” wanda a turance ake ce physics, meaning nature and natural characteristics. Masana sun yi defining physics a harshen Turanci kamar haka: “physics is a branch of science which deals with the study of matter and energy and the relationship between the matter and the energy […]
Ma’anar ittikafi: Ittikafi shine lizimtar masallaci don bautawa Allah Madaukakin Sarki. Hukuncinsa: Sunnah ne, ba ya wajaba sai ga wanda ya yi bakance akansa. Dalilin haka ya tabbata daga Al-Kur’ani da Hadisai da ijma’in malamai. Dalili daga Al-Kur’ani Allah Ya ce: “Kuma mun yi wasiyya ga Ibrahim da Isma’il cewa su tsarkake daki na, saboda masu […]
Tun farko Allah ya halicci maza da son su ga cewa a komi sune kan gaba. Musamman a Arewa inda aka fi sanin cewa a komi namiji ne kan yi jagoranci. Ba kasafai a kan samu macen da ta fi namiji kudi ba, ko a fannonin aikin gwamnati mazan ne kan yi shugabanci, haka a […]
Bismillahi rahmanir Rahim Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Mai Girma da daukaka. Salati da sallama su kara tabbata ga Manzon Allah, da iyalansa da sahabansa. Akwai daga cikin kura-kurai da dama wadanda mai yin azumi kan yi. Ga su nan na kasa su kamar haka: Na farko: Kura-kurai lokacin fuskantar watan Ramadan […]
Kamar yadda muka sani, kowanne abu yana da ginshiƙi watau doron abin da aka ɗora shi yake tafiya yadda ake so. To haka ma fasahar blockchain, an yi mata shisshike da take gudana bisa gare shi. Waɗannan ginshiƙai wajibi ne ga wanzuwar fasahar. Idan babu ɗaya to ragowar sun samu tasgaro, aikinsu zai taƙaita. Waɗannan ginshiƙai […]
Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai. Tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabi Muhammad da alayensa da sahabbansa, da wadanda suka biyo bayansu har zuwa rananr sakamako. A wata makala da ta gabata mun yi bayani akan falalar azumin watan Ramalana inda muka kawo kadan daga cikinsu. A yau za mu duba wasu daga cikin […]
So wani irin yanayi ne da kan sa mutum ya tsinci kansa a cikin wani hali na daban. Sai dai mi? Abu ne shi mai dadi a kuma gefe guda abu ne mai matukar ban tsoro. Duk da kasancewar sa hakan bai zama abin kyama ga mutane ba. Da yawa kan rungume shi da hannun […]
Godiya ta tabbata ga Allah Madaukakin Sarki, tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabi Muhammad, da alayensa da sahabbansa, da wadanda suka biyo bayansu da kyautata. Yana daga hikimar Allah Madaukakin Sarki fifita wasu mutane akan wasu, Ya kuma fifita wasu wurare akan wasu, Ya kuma fifita wasu watanni akan wasu, haka nan kuma […]
Al’umma kalma ce da take nufin jama’a ko kabila da ke zaune a wuri daya tare da amfani da harshe da al’ada iri daya. Sannan yanayin zama kuma, ya danganci yadda mai gida yake zaune da iyalansa, kuma tsarin iyali shi ne ginshikin da aka gina al’ummar Hausa a kansa. Haka zalika a wani bangaren […]
Godiya ta tabbata ga Allah Madaukakin Sarki wanda ya fifita watan Ramadan akan sauran watanni. Tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabi Muhammad da alayensa da sahabbansa, da kuma wadanda suka biyo bayansu har zuwa ranar kiyama. Azumin watan Ramadan na daga cikin ayyukan da Allah Ya wajabta wa bayinsa, kuma rukuni ne daga […]
Mutane da dama suna yawan tambaya dangane da ainihin abin da ake nufi da fasahar blockchain da irin ayyukan da ake iya aiwatar da ita. Masana a wannan fanni suna ta kokarin yin bayani daidai gwargwado, sai dai sarƙaƙiyar da ke cikin ta ya sa da wuya a samu cikakken bayani gama gari dangane da […]
Sunan Littafi: Rayuwarmu Marubuciya: Lubna Sufyan Inda Aka Buga Littafi: Bakandamiya Hikaya Shekarar Bugu: 2022/23 Yawan Babi: 51 Mai Sharhi: Haiman Raees Manufar Sharhi: Bunƙasa Harshen Hausa da ciyar da adabi gaba. Gabatarwa Rayuwar duniyar nan cike take da ƙalubale iri-iri. Yadda duk mu ke tunanin mun gama ganin kowane shafi na rayuwa, matuƙar ba […]
Da yawan maza na ganin mata a matsayin wata halitta mai murdadden hali wacce da wuya ka gane ina ta dosa. Hakan na cima matan tuwo a kwarya kwarai. Mujallar Hivisasa ta kasar Kenya ta gudanar da bincike akan musabbabin hakan. Kadan daga ciki binciken da suka gudanar sun gano cewa hormones din mata na taimakawa wajen halayyarsu, […]
Kwanakin baya nayi ta samu korafi daga bakin mata su na kawo kokensu akan miskilan maza ko in ce miskilin namiji. Da yawa na takaicin halayyar irin wadannan mazaje saboda dabi’arsu ta nuna halin ko in kula. Duk da an san cewa dabi’ar mata ce yawan magana, babban rauninsu a rayuwa shine “So”, sabili da […]
A maƙalar da ta gabata ta dabarun rubutun labari, mun tsaya da bayani ne a kan haɗakar salo sama da ɗaya wajen samar da labari. Mun bayyana yadda ake saƙa salo mabambanta su ƙara armashi a cikin labari, mun kuma faɗi muhimmanci ko amfanin yin hakan. Yau insha Allahu za mu tattauna ne a kan Ɗarsau. […]
Sunan Littafi: Alƙalamin Ƙaddara (1&2) Marubuciya: Lubna Sufyan Inda aka Buga Littafi: Bakandamiya Hikaya (Online) Shekarar Bugu: 2022 Yawan Babi: Littafi na ɗaya: 11, Littafi na biyu: 41; Jimilla: 52 Mai Sharhi: Jamilu Abdulrahman (Haiman Raees) Manufar Sharhi: Bunƙasa Harshen Hausa da ciyar da adabi gaba Gabatarwa Akan ce ka gode wa Allah a kowane […]
A ƙarƙashin kiwon lafiya, kalmar magani sananniya ce ga kowane Bahaushe. Wasu masana, sun yi hasashen cewa, kalmar ba ta rasa nasaba da kalmar ‘gwaji, wato a gwada abu a ga ko zai yi. Suna ganin kalmar ‘hatsin bara’ ce, wato haɗe-haɗen kalmomi ne na Hausa suka samar da ita. Kalmomin su ne: “ma” da […]
Kusan akasarin shafukan labaraina da na dora a Bakandamiya sun cika ka’idojin da ake bukata, kuma Bakandamiya ta biya ni. Sunana Lubna Sufyan, daya daga cikin marubutan da suka saka littafinsu a taskar Bakandamiya, wannan kuma sune hanyoyi ko in ce dabarun da nake bi wajen samun views, comments da kuma ratings bayan na dora […]
Abstract The paper entitled “Madubi Daya Fuska Hudi: Nazari Kan Rikidar Wakar Jarumar Mata Ta Hamisu Yusuf Bureka (Breaker) Ta Fuskar Jigo” This paper is aimed to analyse the changes or adaptation that occurred from the popular poem “Woman Heroine (Jarumar Mata) which is written and sang by famous Hausa poet in modern time Hamisu […]
Hadakar salo shi zamu tattauna a yau. A maƙalar da ta gabata ta dabarun rubutun labari, mun tsaya da bayani ne a kan salon bayar da labari, da kuma yadda marubuci zai riƙa yin rubutu cikin hikima ta yadda zai riƙa goce wa hasashen manazarcinsa wanda ka iya hakaito ƙarshen labarin ya rage masa armashi. […]
Tsakure Wannan takarda mai taken “Hadakar manufa tsakanin ‘yan fim din Hausa na Arewacin Nijeriya da ‘Yan fim din Inglishi na Kudancin Nijeriya” wani yunkuri ne na yin nazarin samuwar hadakar manufa a tsakanin ‘yan fim. A duniyar fina-finai, hadakar manufa ba bakon al’amari ba ne, Akwai irin wannan Hadaka ta manufa ga ‘yan fim […]
A maƙalarmu da ta gabata, mun tsaya da bayani ne a kan salon bayar da labari, inda muka ce salon bayar da labari ya kasu zuwa gida biyu. Akwai salon tauraro cikin fage, da kuma salon tauraro wajen fage. Mun bayyana yadda salon bayar da labari na tauraro cikin fage, wato labarin da ake bayarwa […]
1.0 Gabatarwa Marubuta labarai na amfani da hanyoyi da yawa na bayar da labari ko gina labari a Hausa, sannan duk labarin da za a ba da ko a samar ko a rubuta ko a gina akwai hanyoyin da ake bi domin samun nasarar kai wa ga gaci. Abin lura a nan shi ne babban […]
Sunan Littafi: Abdulƙadir Marubuciya: Lubna Sufyan Inda aka Buga Littafi: Bakandamiya Hikaya (Online) Shekarar Bugu: 2022 Mai Sharhi: Jamilu Abdulrahman (Haiman Raees) Manufar Sharhi: Bunƙasa Harshen Hausa da ciyar da adabi gaba Dangane da marubuciyar An haifi Lubna Sufyan ne a ƙaramar hukumar Ingawa da ke birnin Katsina. Fitacciyar marubuciyar ta fara karatun addini tun […]
Sunan Littafi: Akan So Marubuciya: Lubna Sufyan Inda aka Buga Littafi: Bakandamiya Hikaya (Online) Shekarar Bugu: 2022 Mai Sharhi: Jamilu Abdulrahman (Haiman Raees) Manufar Sharhi: Bunƙasa harshen Hausa da ciyar da adabi gaba Taƙaitaccen tarihin marubuciyar Lubna Sufyan ‘yar asalin ƙaramar hukumar Ingawa ce da ke birnin Katsina. Fitacciyar marubuciyar ta fara karatun addini tun […]
A yau za mu yi bayani ne a akan salon bayar da labari da kuma salon ginin labari. Idan ba ku manta ba, a maƙalar da ta gabata, mun yi bayani game da fa’idar yin bincike a wajen ginin labari, inda muka ce mutunci, ƙima da kuma darajar rubutun marubuci tana zubewa a ƙasa wanwar […]
Sunan Littafi: Dama Sun Fada Mini Marubici: Jibrin Adamu Jibrin Kamfanin Ɗab’i: A. A. Bature Publishers Yawan Shafuka: 200 Shekarar Bugu: 2020 an sake bugawa 2021 Mai Sharhi: Muttaka A. Hassan (Abu Ahmad) Manufar Sharhi: Bunƙasa harshen Hausa da ciyar da adabi gaba. Dangane da marubucin An haife shi a Jos, cikin Nassarawa, unguwar ‘yan […]
A makalar da ta gabata, mun kawo muku bayanin masana game da rubutun zube da kuma matakai daban-daban wanda ka’idojin rubutun Hausa suka bi kafin su kai ga yadda suke a yanzu. Mun tsaya a inda muka ce zamu kawo muku tarihin irin gudumawar da marubutan farko suka bayar, musamman Turawa wajen tubuta littattafai. Tarihin […]
A maƙalunmu na baya, mun tattauna akan abubuwan da suka zama muhimmai marubuci ya sani wajen gina farko-farkon labari, misali gina jigo, salo da makamantansu. Kafin mu ci gaba da abubuwan da suka shafi tsakiyar labari, bari mu duba wani muhimmin abu – zurfafa bincike wajen gina labari. Kamar yadda muka sani bincike wata hanya […]
A maƙalar da ta gabata mun kawo muku yadda ake samar da ganɗoki a labari inda muka yi bayani kuma muka kawo misalan irin yadda ake samar da ganɗokin, wato zaƙuwa da son jin cigaban labari. A maƙala yau, za mu tattauna ne a kan yadda ake samar da baɗoki. Kamar yadda na faɗa tun […]
Tun muna yara ƙanana ake karanta mana labarin da ke littafin Iliya Ɗan Mai Ƙarfi wanda Malam Ahmadu Ingawa ya rubuta kuma kamfanin Gaskiya Corporation ya soma wallafawa a 1951. An ci gaba da wallafa a littafin ƙarƙashin kamfanin NNPC a shekarun 1976 da 1980s har zuwa wannan lokaci da muke ciki ana ci gaba […]
A maƙalar da ta gabata, mun fara yin bayani game da fa’idar samar da ganɗoki a cikin labari, muka ce matsayin ganɗoki da baɗoki a cikin labari, da yadda suke armasa labari, tamkar matsayin dabbobi ne a cikin gidan zoo da irin yadda samuwarsu a ciki yake ƙara wa gidan kwarjini da armashi ga masu […]
Sunan Littafi: Musaddam Ne ZabinaMarubiciya: Safna Aliyu JawabiInda Aka Buga Littafi: Online (WhatsApp)Yawan Shafuka: 180Mai Sharhi: Muttaka A. Hassan (Abu Ahmad)Manufar Sharhi: Bun`kasa harshen Hausa da ciyar da adabi gaba Dangane da marubuciyar Safna Aliyu Jawabi haifaffiyar garin Suleja ce da ke jihar Niger, Nijeriya. Ta fara karatun addini a garin Suleja tun daga yarinta […]
A maƙalar da ta gabatai, mun yi bayani ne game da tsarin murhun girka jigo a labari, inda muka bayyana madogara uku da suka zama kamar duwatsu uku na murhu da idan babu su babu labari. A cikin bayaninmu mun tsaya ne a kan misali na farko a ƙarƙashin dabarun gina farkon labari, inda muka […]
Ƙagaggun labarai na ɗaya daga cikin rukunin adabin Hausawa na zamani, da masana adabin Hausa suka bayyana shi da “zube”, wanda shi ne na farko a cikin rukunin, kafin waƙa da wasan kwaikwayo su zo (Yahaya da wasu, 1992). Shi ƙagaggen labari cike yake da zantukan hira da nishaɗi, wanda ba da gaske ya taɓa […]
A maƙalar da ta gabata, mun yi bayani sosai tare da misalai na yadda ake girka jigo ya koma labari. A yau kuma insha Allahu maƙalarmu za ta yi duba ne a kan irin tsarin murhun da ya kamata a girka jigon a kai. Shin ta wacce mahangar za mu kalli irin wannan hikimar mu samar […]
A makalar da ta gabata na dabarun rubutun labari, mun duba musamman ma’anar jigo da yadda ake samar da jigo. A yau za mu duba yadda ake girka jigo ya koma labari. Da yake mun yi maganar girki, yana da kyau mu yi misali da wani nau’in abincin na Bahaushe da yadda ake girka shi, saboda […]
Bisa sunna ta rayuwa komai yana da mafari ko tushe, kafin ka fara gini kana buƙatar haƙa fandisho, kafin ka yi shuka kana buƙatar huɗa ko saran shuka, amma shi yin rubutu na zube JIGO shi ne abin buƙata na farko kafin komai. Wannan shi ne dalilin da ya sa tunda dabarun rubutu muke so […]
Amfanin zuma yana da yawa bisa fadin masana. Shi dai zuma wani ruwa ne mai zaki, wanda masana a fannin kiwon lafiya suka tantance kuma suka tabbatar da zakinsa bai da wata illa ga jiki ko rayuwar bil’adama. Hasalima dai zuma na samar da kariya ga bil’adama a kan wasu cututtuka daban-daban. Cikin wasu alfanun […]
A ranar 9 ga watan Agusta na 2021 ne wata babbar kotun tarayya da ke birnin Fatakwal ta zartar da hukuncin cewar kuɗin harajin VAT na kayayyaki ba hurumin gwamnatin tarayya ba ne. Dalilin da ta dogara da shi kuwa shi ne, babu wata ayar doka da aka ambaci wannan haraji a ƙarƙashin kundin tsarin […]