March 22, 2019 9:52 PM GMT
KARIN BAYANI AKAN AZUMIN RAJAB.DOMIN AN SHIGAR DA BID'O'I CIKI.
Amma ware ai nufin shi watan rajab d’in da nufin fifita shi ko bashi wata matsayi ta musammam?haqiqa
wannan ba daidai bane.
Nana Aisha (RA) ta ce:
“Manzon Allah (SAW) ya kasance yakan yi
Azumi, harsai mun ce ba zai ajiye ba, kuma
yakan ajiye azumi har sai mun ce ba zai yi
azumin ba, kuma ban tabaganin Manzon Allah ya
cika azumin wata ba face Ramadan, sannan ban
ga watan da Manzon Allah yake yawaitaazumi a
cikinsa ba kamar sha’aban”.
[Ahmad ya ruwaito
Shehun muslunci Ibn Taymiyya yace acikin
littafinsa Majmoo’ al-Fataawa
Akan maganar azumtar Rajab, gabad’ayan
hadisan da suke magana akan haka daeefai ne,
sanan kuma maudooai domin ma’abota sani basu
dogara daga d’aya daga cikinsu ba. Basa daga
cikin hadisai daeefai da suke magana akan
falala. Bayaga kawai mafi yawa daga cikinsu
qarya ce da qage kawai.
Acikin al-Musnad da sauran wurare da akwai
hadisi dake cewa Manzon Allah (s.a.w) yana jin
dadin azumtar watanni masu falala, sune:Rajab,
Dhu’l-Qa’dah, Dhu’l-Hijjah daMuharram, kuma
wannan sai ya had’a da sauran watannin bawai
ware rajab shikad’ai ba.
Ibn al-Qayyim (Allah yaqara masa yarda) yace:
Gabad’ayan hadisin dake magana akan azumtar
watan rajab da yin sallah acikin wasu daga cikin
dararen sa duk qarya ne da qage.
Daga littafin al-Manaar al-Muneef,
Haafiz ibn Hajar yace acikin Tabyeen al-‘Ajab
Babu wani saheehin hadeethi da za’a qirga a
matsayin hujja akan falalar azumtar watan rajab,
ko wani vangare nashi ko kuma sallace tsawon
wani dare nashi.
Shaykh Sayyid Saabiq (Allah ya qara masa
yarda) yace acikin Fiqh al-Sunnah
Azumtar rajab baifi azumtar sauran watanni ba,
face kawai yanadaga cikin watanni mai falala. To
babu wani bayani acikin saheeh sunna dake nuna
wani abu muhimmi akan azumtar watan, haka
duk wani abu da aka ruwaito dangane da wannan
to baikai daidai da za’a daukeshi a matsayin
hujja ba.
Shaykh Ibn ‘Uthaymeen (Allah ya qara masa
yarda) an tambaye shi game da azumtar ashirin
da bakwai na watan Rajab da sallatar wanan
dararen sai yace:
Azumi a ishirin da bakwai d’in watan rajab da
sallatan daren bidi’ah ce sanan dukkan bidi’ah
kuma vata ce.
Allah ya taimakwmu.