A wannan zamani da amfani da na'ura mai kwakwalwa ya zama ruwan dare, kuma fannoni daban-daban na rayuwa suke amfani da shi wajen inganta ayyukansu.
A wannan tafiya ba a bar sashen ilimi a baya ba. Tuni kasashen da suka ci gaba suna amfani da kumfuta da... moreA wannan zamani da amfani da na'ura mai kwakwalwa ya zama ruwan dare, kuma fannoni daban-daban na rayuwa suke amfani da shi wajen inganta ayyukansu.
A wannan tafiya ba a bar sashen ilimi a baya ba. Tuni kasashen da suka ci gaba suna amfani da kumfuta da Intanet wajen inganta ilimi da karatu.
Ina malaman makaranta da masu bincike a fannin koyarwa da karatu, har ma da dalibai, ku zo Bakandamiya ta sama mana farfajiya inda za mu baje kolinmu don koyar da darussanmu ga dalibai ta hanyar amfani da fasahar zamani.
Babu iyakan abinda za mu yi a wannan taska sai iyakan abinda tunaninmu da fasahar da Allah Ya bamu ya tsaya.
Don haka ku shigo wannan zaure mu tattauna, kuma za mu gaya muku hanyoyi daban-daban da za ku iya amfani da Bakandamiya a ajujuwanku da bincikenku, sannan kuma za ku iya kirkiro wasu.
Ku latsa alamar shiga zauren don ku shigo mu tattauna. less
Bakandamiya
(Admin)
GORON JUMMA'A
Assalamu alaikum Malam,
Mutum ya rasu sai ya bar yayye biyu maza, da yayye mata wadanda suke uba daya, da kuma mahaifiyar sa, ya za a raba musu gadon?
Amsa:
Wa alaikum assalam,
Zaβa raba dukiyar kashi shida, a bawa uwa kashi daya, ragowar kashi biyar din a bawa yan'uwa su raba, namiji ya dauki rabon mata biyu.
Amsawa:
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
Daga zauren Fatawowin Rabon Gado Guda 212
Rahmatu Lawan
GORON JUMMA'A
INA YAWAN FITAR DA MANIYYI SABODA MIJINA BA LAFIYA
Tambaya:
Assalamu Alaikum , Dr macece mijinta ba yada lafiyan aure tsawon lokachi, sai ya zamana tana yawan releasing ba sai tayi wani dogon tunani na sha'awaba, ya matsayin ibadarta yake?
Amsa:
Wa alaikumus salam
To gaskiya abin da yake daidai shi ne: ya nemi magani, in kuma bai samu ba, ana iya raba auran, tun da yana daga cikin manufofin aure, katange ma'aurata daga fadawa haramun, kamar yadda shararren hadisinnan ya tabbatar.
Yawan fitar maniyyi zai iya zama lalurar da za ta iya haifar da saukin sharia, saidai na ki ba zai zama lalura ba, saboda iyayenki za su iya wajabtawa mijin neman magani, in kuma bai samu ba, za ku iya rabuwa, Allah ya azurta kowa daΔa falalarsa.
Cigaba da zamanku a wannan halin yana iya jefa ki cikin hadari, mata nawa ne suka zama mazinata ta hanyar wannan sababin?
Ya wajaba ki yi wanka duk sanda maniyyin ya fita, tun da ya fita ne ta hanyar jin dadi.
ALLAH NE MAFI SANI
Daga zauren Filin Fatawa na Dr. Jamilu Zarewa
12/6/1437
Lawan Dalha
Ya Allah Ka sada mu da alkhairan da ke cikin wannan rana; ka tsare mu daga sharri duniya da lahira. #JummaaMubarak
Hadiza Balarabe
Assalamu Alaikum Warahmatullahi Wabarakatuhu
Barkanmu da Safiyar Laraba
*Ya Allah ka kara mana lafiya mai inganci da abinda lafiya zata rayu dashi, Ka yaye mana dukkan abinda ke damunmu na 6oye dana bayyane*
πππAminπππ
Nasiru Yahya
Sama da shekaru 50,marigayi sa'adu Zungur yayi wannan wa'azin a sigar Waka..
~ Matukar a arewa da karuwai,
~ yan daudu dasu da magajiya.
~ Da samari masu ruwan kudi,
~ Ga mashaya can a gidan giya.
~ Matukar yayan mu suna bara,
~ Titi da Loko-lokon Nijeriya.
~ Hanyar birni da na kauyuka,
~ Allah baku mu samu abin miya.
~ Sun yafu da fatar bunsuru,
~ Babu mai tanyonsu da dukiya.
~ Babu shakka yan kudu zasu hau,
~ Dokin mulkin Nijeriya.
~ In ko yan kudu sunka hau,
~ Babu sauran dadi, dada kowa zai
sha wuya.
~ A Arewa zumunta ta mutu,
~ Sai karya sai sharholiya.
~ Camfe-camfe da tsibbace
tsibbacen,
~ Malaman karya yan damfara.
~ Sai karya sai kwambon tsiya,
~ Sai hula mai annakiya.
~ Ga gorin asali da na dukiya,
~ Sai kace dan annabi fariya.
~ Jahilci ya ci lakar mu duk,
~ Ya sa mana sarka har wuya.
Ya sa mana ankwa hannuwa,
~ Ya daure kafarmu da tsarkiya.
~ Bakunan mu ya sa takunkumi,
~ Ba zalaka sai sharholiya.
~ Wagga al’umma mai zata yo,
~ A cikin zarafofin duniya.
Kai Bahaushe ba shi da zuciya ,
~ Zaya sha kunya nan duniya “.
~ “Mu dai hakkin mu gaya muku,
~ Ko ku karba ko kuyi dariya.
~ Dariyar ku ta zam kuka gaba,
da nadamar mai kin gaskiya.
~ Gaskiya ba ta neman ado,
ko na zakin muryar zabiya.
~ Karya ce mai launi bakwai,
ga fari da baki ga rawaya.
~ Ga kore ga kuma algashi,
toka-toka da ja sun garwaya”.
~ Marigayi Sa’adu Zungur a cikin
~ waken sa mai suna “Arewa
~ Jamhuriya ko Mulukiya”
Allah Yajikan Malam Saadu Zungur
Allah kayimasa Rahama amin amin