A wannan zamani da amfani da na'ura mai kwakwalwa ya zama ruwan dare, kuma fannoni daban-daban na rayuwa suke amfani da shi wajen inganta ayyukansu.
A wannan tafiya ba a bar sashen ilimi a baya ba. Tuni kasashen da suka ci gaba suna amfani da kumfuta da... moreA wannan zamani da amfani da na'ura mai kwakwalwa ya zama ruwan dare, kuma fannoni daban-daban na rayuwa suke amfani da shi wajen inganta ayyukansu.
A wannan tafiya ba a bar sashen ilimi a baya ba. Tuni kasashen da suka ci gaba suna amfani da kumfuta da Intanet wajen inganta ilimi da karatu.
Ina malaman makaranta da masu bincike a fannin koyarwa da karatu, har ma da dalibai, ku zo Bakandamiya ta sama mana farfajiya inda za mu baje kolinmu don koyar da darussanmu ga dalibai ta hanyar amfani da fasahar zamani.
Babu iyakan abinda za mu yi a wannan taska sai iyakan abinda tunaninmu da fasahar da Allah Ya bamu ya tsaya.
Don haka ku shigo wannan zaure mu tattauna, kuma za mu gaya muku hanyoyi daban-daban da za ku iya amfani da Bakandamiya a ajujuwanku da bincikenku, sannan kuma za ku iya kirkiro wasu.
Ku latsa alamar shiga zauren don ku shigo mu tattauna. less
Hadiza Balarabe
Wata budurwa nahango tsaye Bakin titi da Jan kaya da farin hijab dagani makaranta zata
Hmm FAUZA YAR WANKA kenan
kubiyomu donjin ya zata kaya zata MAKARANTAR kuwa?
https://youtu.be/BZsKZJhHjOU
Nasiru Yahya
Sama da shekaru 50,marigayi sa'adu Zungur yayi wannan wa'azin a sigar Waka..
~ Matukar a arewa da karuwai,
~ yan daudu dasu da magajiya.
~ Da samari masu ruwan kudi,
~ Ga mashaya can a gidan giya.
~ Matukar yayan mu suna bara,
~ Titi da Loko-lokon Nijeriya.
~ Hanyar birni da na kauyuka,
~ Allah baku mu samu abin miya.
~ Sun yafu da fatar bunsuru,
~ Babu mai tanyonsu da dukiya.
~ Babu shakka yan kudu zasu hau,
~ Dokin mulkin Nijeriya.
~ In ko yan kudu sunka hau,
~ Babu sauran dadi, dada kowa zai
sha wuya.
~ A Arewa zumunta ta mutu,
~ Sai karya sai sharholiya.
~ Camfe-camfe da tsibbace
tsibbacen,
~ Malaman karya yan damfara.
~ Sai karya sai kwambon tsiya,
~ Sai hula mai annakiya.
~ Ga gorin asali da na dukiya,
~ Sai kace dan annabi fariya.
~ Jahilci ya ci lakar mu duk,
~ Ya sa mana sarka har wuya.
Ya sa mana ankwa hannuwa,
~ Ya daure kafarmu da tsarkiya.
~ Bakunan mu ya sa takunkumi,
~ Ba zalaka sai sharholiya.
~ Wagga al’umma mai zata yo,
~ A cikin zarafofin duniya.
Kai Bahaushe ba shi da zuciya ,
~ Zaya sha kunya nan duniya “.
~ “Mu dai hakkin mu gaya muku,
~ Ko ku karba ko kuyi dariya.
~ Dariyar ku ta zam kuka gaba,
da nadamar mai kin gaskiya.
~ Gaskiya ba ta neman ado,
ko na zakin muryar zabiya.
~ Karya ce mai launi bakwai,
ga fari da baki ga rawaya.
~ Ga kore ga kuma algashi,
toka-toka da ja sun garwaya”.
~ Marigayi Sa’adu Zungur a cikin
~ waken sa mai suna “Arewa
~ Jamhuriya ko Mulukiya”
Allah Yajikan Malam Saadu Zungur
Allah kayimasa Rahama amin amin
Mukhtar Musa Karami Abu Hisham
Cinikin mutum ake kamar yanda ake cinikayya a kasuwa,farashi suke yanke wa kamar yanda ake yi a super market,basa yin ragi balle su nuna alamar sauki,idan ka biya kudi su baka,idan ka ki biya su kasheshi.
Basa tsoron kowa,balle su yi tunanin akwai wanda zai iya tunkararsu,dole akwai abin tsoro fa,kasar nan ta mu akwai firgici sosai,Ya Allah ka karemu daga wannan masifar ta satar mutane.
Allah ka bamu lafiya da zama lafiya amin