• Contrast
    • Font
    • A
  • Sign In
  • Sign Up
    Loading ...
View All Updates Mark All Read
Bakandamiya
  • Home
  • Rubutu
  • Bidiyoyi
  • Sautuka
  • Hotuna
  • Zauruka
  • Profile Type: Personal
  • Profile Views: 9,229 views
  • Followers: 47 followers
  • Last Update: April 1, 2021
  • Last Login: April 17, 2021
  • Joined: November 21, 2017
  • Member Level: Basic
  • Update
  • About

Update

The post was not added to the feed. Please check your privacy settings.
  • Maishaq Muhammad
    Maishaq Muhammad liked Zaharadden Nasir's post.
    April 1, 2021
    Zaharadden Nasir
    Faษ—uwa, ba dalili bane da zai sa kaฦ™i sake gwadawa...

    ฦ˜ARA GWADAWA
    • 4 people like this
    • Maishaq Muhammad
      Lawan Dalha Gaskiya ne wannan \uD83D\uDC4C
      • March 31, 2021
      • -
      • 1 likes this
      • -
      • Report
    • Maishaq Muhammad
      Zaharadden Nasir Na gode da yabawa yallaษ“ai\uD83D\uDC4D
      • April 1, 2021
      • -
      • 1 likes this
      • -
      • Report
    • Maishaq Muhammad
      Lawan Dalha Godiya nake, Deeny.
      • April 5, 2021
      • -
      • Report
  • Maishaq Muhammad
    Maishaq Muhammad liked ASEE BEAUTY's post.
    April 1, 2021
    ASEE BEAUTY
    Muna mika ta'aziyarmu ga Ummyter Abdallah bisa ga rashin mahaifinta da ta yi.

    Allah Ya jikansa da rahma, Ya sa mutuwa hutu ce a gare shi.
    • 5 people like this
    • Maishaq Muhammad
      Hafsat Tukur Amin
      • March 31, 2021
      • -
      • Report
    • Maishaq Muhammad
      Lawan Dalha Amin Ya Rabb
      • March 31, 2021
      • -
      • Report
    • Maishaq Muhammad
      Rahmatu Lawan Amin Ya Allah
      • April 1, 2021
      • -
      • Report
  • Maishaq Muhammad
    Maishaq Muhammad liked ASEE BEAUTY's photo.
    April 1, 2021
    Ga kyau ga arha
    • 6 people like this
    • Maishaq Muhammad
      Umar1984 price
      • March 31, 2021
      • -
      • Report
    • Maishaq Muhammad
      ASEE BEAUTY 10k
      • April 6, 2021
      • -
      • Report
  • Maishaq Muhammad
    Maishaq Muhammad commented on Abubakar Sulaiman II's photo.
    April 1, 2021
    Meyasa ta bari Buhari ya tafi London? Kokuma wannan dafa'in na Talakawa me kurum? ๐Ÿค”๐Ÿค”๐Ÿค”๐Ÿค”
    • Rahmatu Lawan, Bakandamiya, and Lawan Dalha like this.
    • Maishaq Muhammad
      Maishaq Muhammad Toh wa ya sani? Kai Dai Kaga Mutum ka Kuma yi hankali da mutum! Kila bata ma San zai tafi landan din ba!
      • April 1, 2021
      • -
      • 1 likes this
      • -
      • Report
  • Maishaq Muhammad
    Maishaq Muhammad liked Rahmatu Lawan's post.
    April 1, 2021
    Rahmatu Lawan shared Ayeesh Chuchu 's blog.
    • 7 people like this
  • Maishaq Muhammad
    Maishaq Muhammad liked Nafisat Isma'il's post.
    April 1, 2021
    • 4 people like this
  • Maishaq Muhammad
    Maishaq Muhammad liked Nafisat Isma'il's post.
    April 1, 2021
    Nafisat...  moreNafisat Isma'il
    ๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚
    ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ
    ๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡
    ...  more๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚
    ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ
    ๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡
    *RAUDHA*
    ๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡๐Ÿ‡
    ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ
    ๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚๐Ÿ‚

    *MALLAKAR๐Ÿ˜—โœ๏ธ
    _Nafisat Isma'il Lawal Goma._

    *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*๐Ÿง๐Ÿป‍โ™€๏ธ


    *ุจุณู… ุงู„ู„ู‡ ุงู„ุฑุญู…ู† ุงู„ุฑุญูŠู…*


    *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*๐ŸŒž

    ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN  OUR READERS ๐Ÿ’ช)```

    /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

    *P.W.A*โœ๏ธ


    *JIKAR LAWALI CE*โœ๏ธ

    *Wattpad: UmmuDahirah*๐Ÿ‘ˆ




    .


    *NOT EDITED* ___________________________๐Ÿ“—


    *SEASON FORTY ONE*


    _______๐Ÿ“– Biri da wando ta saka me santsi Light orange, ฦ™asan wandon me fela ne sosai, sai ta saka top fari iya gwiwar ta, me kwalliyan stones, sannan sai ta naษ—a blue ษ—in ษ—ankwali a kanta, wanda ya fito mata da gashin ta ta ฦ™asan ฦ™eya, Light makeup tayi da ya fito da tsantsan kyawun ta, kai Masha Allah duk wanda ya ga RAUDHA wannan lokacin bazai so ya ษ—auke idanun sa ba, ta haษ—u iya haษ—uwa sai wanda ya gani, takalmin da ta saka me tsinin gaske ne cover me igiya, kalan Light blue da farin Socks a ciki, sai tashin ฦ™amshi take yi irin turaren nan na Arabian


    Ramcy dake zaune saman sofan ษ—akin ta, sakin baki tayi tana kallon ta


    Sai da RAUDHA ta matso kusa da ita, ta sanya hannun ta ta shafa fuskar ta tana murmusawa. Sannan a time ษ—in Ramcy ta rufe bakin ta bayan ta dawo da tunanin ta jikin ta


    "What happened Besty?"


    Gwauron numfashi Ramcy ta sauke kafin tace, "ban san me zan ce bane wlh Besty, haษ—uwar ki yayi yawa. Masha Allah gaskiya ki gode Allah".


    Murmushin ta me kyau ta saki kafin ta lumshe ido ahankali ta furta, "Shukran Lak, linazhab".


    Da ido Ramcy tayi mata magana, "wai what?"


    "Let's go".


    Miฦ™e wa Ramcy tayi tana gyara zaman gyalen ta, itama tayi shiga ne cikin baฦ™in yadi me santsi, ษ—inkin doguwar riga, duk da kasancewar ta baฦ™a but sosai tayi kyau matuฦ™a, kasancewar an yi wa rigan ado da jan zare sai Stones, kuma tayi amfani da jan ษ—ankwali ne sai farin gyale.



    Fita suka yi, inda tuni an gama taruwa su kaษ—ai ake jira a wajen. A hanya suka haษ—u da Farida ta zo kiran su, sai suka tafi tare, itama kanta sai ya ba kwalliyan RAUDHAN take yi


    Ita kuwa sai murmushi take saki me fid da sihirtaccen kyawun ta, tana takun nan nata ษ—ai-ษ—ai me ban sha'awa, kasancewar bata yafa gyale ba, shiyasa duk inda jikin ta ya juya ana ganin komi ta yanda take sarrafa jikin ta.


    Tun doso wan su wajen sai idanun mutane kawai ya koma kanta, hakan yasa wasu da hankalin su be kai kanta ba, sai duk suka kallo wajen


    Tana tsakiyar Farida da Ramcy ne, suna taho wa wajen


    Nan da nan aka soma tafi sabida sanar wan da MC ke yi na zuwan ta, nan ya soma koษ—a ta yana kambama ta


    Ita kuwa idanuwan ta na kan su Daddy da ta hange su, su ma suna mata murmushi, Suhaib har da ษ—aga mata babban yatsan sa alamun tayi zam-zam. ita kuwa ta saki murmushin nan da ke ฦ™ara wa fuskar ta kyawu.



    "Kai man juyo ka ga wata halitta don Allah". Cewar Sharif da yayi maganar a hankali kusa da kunnen Zulain dake waya ya karkace kai


    Juyo wa yayi kuwa, yana shirin hararan sa sai idon sa suka sauka kan RAUDHA dake tafiya zuwa wajen zaman ta, take anan komi nasa ya tsaya illa idanun sa da ya lumshe ya sake buษ—e wa akanta, yana son tabbatar wa kansa itan ce ko kuwa?. Maganar Sharif ya sake dawo da shi hayyacin sa


    "Ni wlh da na san S. Makamashi yana da ฦ™anwa irin wannan, ai da tuni ita na nema, me zai kai Ni zuwa waje gida be ฦ™oshi ba".


    Shiru Zulain yayi don hankalin sa be gama dawo wa kan Sharif ba, bare ya tantance me yake faษ—a, idanun sa ฦ™yam akan RAUDHA har ta zauna ta yanda yanzu yake ganin fuskar ta sosai. A take ya saki wani irin ajiyan zuciya yana sake lumshe ido


    A tare Sharif da Mom ษ—in sa da suke waya, suka je ho masa tambaya the same


    Buษ—e idanun sa yayi yana kallon Sharif da ya tsaya kallon sa shima, sai kuma yayi saurin kara wayan a kunnen sa sosai yana faษ—in, "Mom zan kira ki letter please". Ya Yi saurin katse wayan be jira cewar ta ba, nan ya sake mayar da idanun sa kan RAUDHA gaba ษ—aya ya mayar da hankalin sa gare ta, sosai yaji daษ—in ganin ta da baki ma bazai iya furta wa ba, har wani sakin murmushi yake yi batare da ya sani ba


    Sharif dake faman kallon sa baki sake, ya jinjina kansa ya ce, "cab ษ—ijam.. Kar dai har ta sace maka zuciya daga kallon farko?"


    Zulain be kalle sa ba don ba ya son abunda zai gilma ga kallon kyakykyawar nan, amma kuma sai ya ษ“ata fuska yana kumbura shi irin maganar Sharif ษ—in fa ya fara isar sa


    Murmushi kawai Sharif yayi be ce komi ba, ya mayar da hankalin sa shima ga abinda ake yi.



    A lokacin RAUDHA ta miฦ™e ne tana speech da muryan ta me daษ—i da ya karaษ—e wajen. Sosai duk mahalukin dake wajen ya mayar da hankalin sa gare ta cike da sha'awa. Har ta gama aka soma mata tafi Raf.. Raf... Raf


    Sannan sai Suhaib ya amsa ya sake ma kowa godiya tare da yaba wa ฦ™anwar sa, da nuna irin tsantsan ฦ™aunar da yake mata. daga nan kuma Daddy ne ya amsa shima ya soma yabon ta sosai, da abun mamakin da ta ba su, tare da nuna wa mutane tsantsan alfaharin da yake yi da ษ—iyar sa


    Haka ake ta tafa wa cike da tsananin burge su da suka yi, don sosai iyalan suka burge kowa. Haka dai aka ci gaba da gudanar da partyn cike da sha'awa, inda daga baya MC ya kira RAUDHA domin ta taka


    Murmushi kawai ta soma zuba wa, domin har yanzu ฦ™aunar ta da rawa yana nan, sai dai yanzu ba kamar da ba, duk da a yanzu ta koyo irin rawan larabawa ne, ko tana yi zaka ka bata cika yin irin na nan ba saboda ya zame mata jiki na larabawan. Tashi tayi ta fita ta soma taka wa a hankali tana dariya bakin ta ya ฦ™i rufuwa


    Nan Suhaib ya taso ya soma taya ta


    Yanda yake rawan ne sai da ya ba kowa dariya, sai tafi ake musu


    Ita RAUDHA ta saka a sauya musu, don ta kasa yi sosai sabida waฦ™ar Hausa ce, sai ta ce a saka mata na Laraba wa, ai nan ta soma taka wa irin nasu sosai, sai shima Suhaib ya biye mata suna yi tare, har da riฦ™e hannu irin na laraba wa yanda suke yi


    Sosai yanzu ษ—in Suhaib yafi ba wa kowa dariya, kowa ka gani wajen nishaษ—i yake yi.



    Lumshe idanu Zulain yayi saboda tsantsan wani farin ciki da yake ziyartan sa, sosai yarinyan ta matuฦ™ar burge sa fiye da tunanin mutum, nan da nan ya ji soyayyar ta me tsananin ฦ™arfi ya kama sa. Har wani buga tagumi yayi da hannu biyu yana bin ta da kallo.


    While sauran samarin, abokan Suhaib duk haka ne a wajen su, kowa fatan sa ya dace da mallakan kyakykyawar balarabiyyan nan.







    ๐ŸŒ๐ŸŒ๐ŸŒ๐ŸŒ๐ŸŒ๐ŸŒ๐ŸŒ๐ŸŒ๐ŸŒ๐ŸŒ


    Wata farar mota ce ta shigo cikin gidan a wannan lokacin, ahankali motan take tafiya har zuwa inda akayi parcking motoci, kamar mintuna biyu da tsayuwar motan aka buษ—e ฦ™ofan, sai dai wanda ke ciki be fito ba, illa ziro fararen ฦ™afafuwan sa dake cikin baฦ™in sandal Shoes da yayi waje


    Daga inda yake duk da akwai tazara sosai da inda ake partyn, amma kuma hakan be sa tattausan waฦ™ar larabawan dake tashi a wajen kasa ratsa masa kunnuwa ba, take anan ya lumshe idanun sa cike da jin daษ—in waฦ™an, kamar shuษ—ewar mintuna biyar ya buษ—e su yana aza idanun sa kan wayan sa dake saman cinyan sa, ษ—auka yayi ya soma dubo Numban Suhaib da yayi masa serving da Dude yayi kira


    While Suhaib na filin rawa yana tiฦ™an rawa tare da RAUDHA, sai yaji wayan sa na ruri, dasauri ya saki hannun ta yana zira wa cikin aljihu ya ciro wayan, ganin sunan Dude a screen ษ—in wayan na yawo, sai nan da nan fara'an sa ya ฦ™aru, matsawa yayi gefe yana answer call ษ—in ya kara a kunne, "Dude".


    "Surprise! Gani a cikin gidan ku".


    Waro ido Suhaib yayi, "haba don Allah".


    Murmushi yayi shi kuma yace, "ka zo ka gani, ina nan wajen parcking space". Daga haka ya katse wayan


    Da sauri Suhaib yayi hanyar barin wajen


    Inda RAUDHA ta kira sunan sa


    Juyo wa yayi yana kallon ta. Ta ษ—age masa gira akan "ina zai je?"


    Nuna mata yayi da hannu wai "yanzu zai dawo".


    Ta marairaice fuska kafin ta juya ta nufi wajen zaman ta. A lokacin ne aka soma bata kyaututtuka.




    ๐ŸŒ๐ŸŒ๐ŸŒ

    Suhaib na isa wajen parcking space, Rayyan dake mota ya fito yana rufe wa. Rungume juna suka yi cike da tsananin murna, kafin kuma su saki juna suna cafe hannayen su ko wanne baki a washe


    "Dude wlh ka shammace Ni, nayi tunanin ba yanzu zaka dawo ba".


    Murmushi Rayyan yayi yace, "dama wannan week ษ—in zan shigo, but sai naga dacewar shigowa yau ษ—in tunda naga yau ce ranan ฦ™anwar ta mu, sai in Taya ta murna".


    Dariya Suhaib ya saki yana ฦ™ara ba shi hannu suka cafe yace, "gaskiya ka kyauta, Daddy zai yi farin ciki da zuwan ka, to ya Uncle da Ammee, da su Faruk?"


    "Alhmadulillah duk suna gaishe ku, akwai babban surprise ma, but bazan sanar maka ba sai muna gaban Daddy".


    Murmushi Suhaib yayi yace, "ok mu je to, mun tsaya a nan".


    Jan hannun sa yayi suka nufi cikin gidan. Har sun kusa ฦ™arisa wa wajen taron sai wayan Rayyan tayi ฦ™ara, ogan sa ke kiran sa don haka yace ma Suhaib "yayi gaba zai zo". Wayan ya ษ—auka suka soma magana. Daga inda yake yana hango taron mutanen, inda fitilu masu haske suka haske wajen, kasancewar duhun magriba ta gabato, a time ษ—in ma shirin tashi suke yi.


    Yana gama wayan sai ya nufi wajen, a time ษ—in har wasu sun soma barin wajen sabida an gama.


    Tuni itama RAUDHA taja hannun Ramcy sun shige gida.


    While su Daddy sun tsaya suna sallama da mutane.


    ฦ˜arisawa Rayyan yayi wajen Suhaib.




    ๐ŸŒ๐ŸŒ๐ŸŒ


    Kai tsaye ษ—akin RAUDHA dake sama suka wuce, anan suka zube kan kujera kowa na faษ—an gajiyan da ya sha, sai kuma Ramcy ta tashi tana faษ—in, "oh na bar su Aunty Nafeesa a waje, kuma sun ce min tafiya za su yi, ina zuwa bari inje".


    RAUDHA tace, "miฦ™o min wayan ki, but kar su tafi yanzu zan sauko sai mu gaisa, in yaso drever ya mayar da su, but ke nan zaki kwana ko?"


    Dariya Ramcy tayi tana zaro ido, "No ai nima tafiya zan yi zuwa anjima kaษ—an, sabida Baba na gari kuma sai da yayi min gargaษ—in in dawo, ina tunanin ma zamu tafi tare kawai da su ne".


    "Ok mu je to sai mu yi sallama". cewar RAUDHA tana miฦ™e wa tare da wayan ta dana Ramcy dake hannun ta


    Ramcy kuma ษ—aukar jakan ta tayi suka fice.



    RAUDHA tafiya take yi tana latsa wayoyin, kasancewar tana son tura pictures and videos ษ—in da Ramcy tayi mata ne a wayan ta, kuma tana son tura wa *ฦ˜alby* a yanzu ษ—in.


    Sai da suka fita waje, kafin suka haษ—u da su Amarya da Aunty Nafeesa suna shirin shigowa


    Anan RAUDHA tayi musu godiya sosai, inda tasaka masu aiki suka kwaso musu kayan party ษ—in. har wajen motan da za'a tafi da su ta raka su, kasancewar gaba ษ—aya an gama watse wa, wasu sun wuce masallaci.


    Su sun shiga mota, ita kuma ta tsaya da Ramcy suna ษ—an Surutu, har sanda ta gama tura wa kafin ta miฦ™a mata wayan. Sai da ta jira suka tafi tana ษ—aga musu hannu kafin ta juyo cikin gidan. Da ษ—an tazara tafiyan, ahankali take taka wa tana latsa wayan ta, inda take karanta text ษ—in da ฦ˜albyn ta ya turo mata, tana sakin murmushi cike da nishaษ—i, har sanda ta iso cikin gidan, ta hau Lifter ya wuce da ita sama. ษ—akin ta takoma ta shiga Toilet tayi wanka kafin ta ษ—auro alwala, kayan ta ta saka farar less mara nauyi tamkar yadi, doguwar riga akayi mata fitet amma me guntun hannu, sai ta tufke gashin ta ta saka hula Robber ja, ta ษ—aura Hijab tayi Sallah, sai da ta gama ta cire ta ษ—auki wayan ta tafito parlour'n sama, anan ta haษ—u da Farida da yaran ta tana buษ—e musu Chocolates suna sha


    "My guys how far?" RAUDHA tayi maganar tana murmushi bayan da ta ฦ™ariso wajen su


    Nan suka tashi suka nufo ta, sai ta soma ba ma Abdul hannu suka cafe, sai kuma ta miฦ™a wa Haneep da ya miฦ™o mata nasa yana dariya da zilalar da yawu


    Murmushi tayi ta saka nata hannun cikin nasa, sannan ta sumbaci goshin sa ta ce, "My Daddy , I love you so much".


    Washe baki yayi cike da murna, cikin muryan sa da ba ya fita maganar sosai ya ce, "I lobi u Baby".


    Shima wai yayi irin na Suhaib da yake kiran ta Baby


    Sai suka saka mishi dariya daga ita har Farida dake kallon su


    "Wow My Daddy wa ya koya maka faษ—an suna na?"



    Abdul yayi saurin cewa, "Aunty ai yaji Daddy na faษ—a miki ne, kuma yanzu yace mu kira ki, sai ya ce miki i love You Baby, shi ne shima ya faษ—a, but be iya sanar da ke sauran ba".


    Murmushi RAUDHA tayi ta shafa kan Abdul tana faษ—in, "kai kuma me wayau ga shi ka faษ—a".


    Ya washe baki yana tsalle


    Still murmushin tayi; tayi musu peck a kumatu, sanan ta shafa kansu, ta miฦ™e tana kallon Farida tace, "Aunty bari in zo".


    Tashi za su yi su bi ta, sai Farida ta riฦ™e su tana ce musu "su zo ta gama ษ“are musu biscuits and Chocolates ษ—in".



    RAUDHA tuni ta bar wurin, ta Steps ta nufi ฦ™asa, a hawa na biyu ta tsaya ta shiga parlour'n don duba Daddy, don tasan baza su wuce suna nan ba dukan su. Tana shiga wani ฦ™amshi ya doki hancin ta, lumshe ido tayi tana buษ—e wa, tabbas kamar ta taษ“a sanin me turaren nan, kamar ta taษ“a jin sa a wani waje, amma aina? Wurga idanu ta soma yi cikin parlour'n. Can ta hangi mutum saman kujera, sai dai bayan sa take hanga tunda kujeran da ya zauna a kai ya juya wa ฦ™ofa baya ne


    Kamar ta wuce sai kuma wani zuciyan nata ya bata umarnin zuwa ta ga ko waye, domin dai tana ji a ranta ta san koma waye ne, kuma farin sani tunda turaren sa ya tabbatar mata da hakan, amma kuma ta kasa tuna inda ta sani. Takowa tayi ta nufo wajen


    Kasancewar bata da takalmi a ฦ™afafuwan ta sai Socks, shiyasa Rayyan be San da zuwan ta ba, ya ฦ™uฦ™e sai kallon zafafan hotunan ta da ta turo masa yake yi, yana zuba murmushi



    Gab ta kusa isa wajen, inda ฦ™iris ya rage ta hangi abinda yake yi a wayan, sai ya juyo da sauri, sabida ajikin sa sai da yaji kamar da mutum a wajen, kuma take yaji ฦ™amshin turaren ta ya bugi hancin sa.


    Haษ—a idon da suka yi, sai ta tsaya cakkk tana bin sa da kallo, ฦ™ure sa da idanu kawai tayi ta kasa tunanin komi


    Haka zalika shima idanun ya zuba mata, yana kallon ta cike da tsantsan ฦ™auna a idanun nasa, tare da tsatsan kewar ta gami da muradin ta cikin ransa. Komi nata ya sauya fiye da Da, ta sake girma da tsananin kyau.  less  less
    • 4 people like this
  • Maishaq Muhammad
    Maishaq Muhammad liked Mustapha musa abu Aisha's post.
    April 1, 2021
    Mustapha musa abu Aisha
    FALALAR ZIKIRI DA AMFANIN SA.

    1. Yawan zikri yana korar...  more
    Mustapha musa abu Aisha
    FALALAR ZIKIRI DA AMFANIN SA.

    1. Yawan zikri yana korar sheษ—an
    2. Yawan zikri yana jawo samun yardar...  moreFALALAR ZIKIRI DA AMFANIN SA.

    1. Yawan zikri yana korar sheษ—an
    2. Yawan zikri yana jawo samun yardar Allah
    3. Yawan zikri yana gusar da damuwa da baฦ™in ciki daga zuciya
    4. Yawan zikiri yana jawo farin ciki da annushuwa da nasaษ—i a zuciya
    5. Yawan zikiri yana ฦ™arfafa zuciya da jiki.
    5. Yawan zikiri yana haskaka fuska da zuciya
    7. Yawan zikri yana jawo arziki
    8. Yawan zikri yana jawo samun kwarjini da jin dadi da farin jini
    9. Yawan yana jawo samun ฦ™aunar Allah ta'ala, samun ฦ™aunar Allah shine babban buri.
    10. Yawan zikri yana jawo kusanci da Allah, har a wayi gari mutum ya samu matsayin ihsani.
    11. Yawan zikri yana jawo komawa zuwa ga Allah ta'ala, cikin farin ciki
    12. Yawan zikri yana buษ—ewa mutum kofa ta samun yarda, da kusanci (Alฦ™urbiyya) tsakanin sa da Allah ta'ala.
    13.. Yawan zikri yana buษ—ewa mai yinsa babun ilmi, duk sanda ya yawaita ambaton Allah, zai ฦ™ara sanin Allah ta'ala.
    14. Yawan zikri yana buษ—ewa mutum matsayin ganin buwayar Allah ta'ala, da isar sa.
    15. Yawan zikri zai sa Allah ya ambaci mai yawan yi, duk sanda ya Ambani Allah, shima zai ambace shi.
    16. Yawan zikri yana raya zuciya domin zikri ga zuciya kamar kifi ne a cikin ruwa, yaya kifi yake kasancewa idan aka raba shi da ruwa? Haka mutum zai kasance idan baya ambaton Allah ta'ala.
    17. Yawan ambaton Allah yana zama kamar abinci ga zuciya da rai.
    18. Yawan zikri yana washe zuciya ya goge tsatsa daga cikin zuciya.
    19. Yawan zikri yana kankare zunubi
    20. Yawan zikri yana kare mutum daga ษ—imuwa da gafala.
    21. Yawan zikri idan yana tuna Allah a cikin yalwa da wadata , Allah zai fidda shi daga cikin halin tsanani.
    22. Yawan zikri yana tsaratarwa daga saukar azaba.
    23. Yawan zikri yana jawo saukar nutsuwa da saukar rahma, da lulluษ“ewar Mala'iku,
    24. Yawan zikri yana shagaltar da harshe ga barin giba da gulma da ฦ™arya Annamimanci, da ashariya.
    25. Majalisin da ake zikri, sheษ—an baya zama a wajan
    Albarka tana sauka a Majalisin da ake zikiri.
    26. Yin zikri yana kare mutum daga hasarar lokaci, da tashi da warin mushen jaki daga majalisi.
    27. Duk wanda ya ambaci Allah a ษ“oye, har ya yi hawaye don ganin girman Allah, zai shiga inuwar al'arshi ranar Alฦ™iyama.
    28. Idan yawan zikri ya ษ—aukewa mutum hankali, har ya zama baya rokon wata bukata, Allah zai bashi fiye da dukkan masu roฦ™o suka roฦ™a.
    29. Zikri shine mafi saukin ibada mara wahala kuma ga yawan lada.
    30. Daga cikin falalar zikiri, yana jawo a dasawa mutum bishiya a gidan Aljanna, kamar yadda yazo a hadisi, Duk wanda ya ce Subhanallahil azeem wa bihamdihi.
    31. Daga cikin falalar zikri, Kalmomi guda biyu masu saukin faษ—a akan harshe masu nauyi akan sikeli, abin ฦ™auna a wajan Allah, Subhanallahi wa bi hamdihi subhanallahil azeem.
    32. Dawwama a cikin zikiri yana ฦ™are mutum daga taษ“ewa.
    33. Zikri yana zama a kowane hali, babu sharaษ—in sai da Alwala ko tsarki.
    34. Yawan zikri haske ne, a duniya da ฦ™abari da makoma da siraษ—i.
    35. Yawan ambaton Allah shine tushen komai, idan ka sami arziฦ™in yawan sa ka gama sumun dukkan komai daga Allah.
    36. Zikri yana kusanta abinda yake nesa, na buฦ™atu kuma yana nisanta abinda yake kusa, na damuwa da baฦ™in ciki.
    37. Zikri yana tashin zuciya daga baccin gafala.
    38. Yawan zikri yana jawo samun ษ—anษ—ano mai faranta rai.
    39. Mai yawan ambaton Allah, kada ka damu domin Allah yana tare da kai.
    40. Yawan zikri yayi daidai da fita yaฦ™i da ciwar da dukiya mai yawa.
    41.. Ambaton Allah shine tushen nuna godiya ga Allah, domin duk wanda baya zikri baya godiya.
    42. Zikri yana jawo samun ni'ima daga Allah kuma yana tunkuษ—e Sakar fushin Allah. Mafi darajar mutane a wajan Allah shine wanda harshen sa ya zamo ษ—anye a wajan ambaton Allah ta'ala.
    43. Allah ta'ala da Mala'ikun sa suna yin salati ga mai yawan ambaton Allah.
    44. Yin zikri shine Asalin samun soyayyar Allah da tsira daga faษ—awa cikin maฦ™iya Allah ta'ala.
    45. Yawan zikri yana jawo a sami katon dausayi a cikin aljanna.
    46. Majalisin zikri wajan zaman Mala'ikun Allah ne.
    47. Dukkan ibadu da Allah ya yi umarni a yi babbar Manufar su shine yawan ambaton Allah.
    48. Dukkan ibadar da ake ambaton Allah da yawa a ciknsa tafi dukkan sauran ibadu kamar sallah bayan Tauhidi.
    49. Yin zikri yana tsayawa a matsayin Sadaฦ™a da Aiyukan lada da ake yi da dukiya.
    50. Ambaton Allah yana ฦ™ara ฦ™arfin imani.
    51. Yawan zikri yana sauฦ™aฦ™ewa mutum duk wani abu mai wahala.
    52. Yawan zikri yana jawo zaman lafiya da kwanciyar hankali.
    53. Zirki yana zama kariya daga sharrin magauta da maฦ™iya, musamman zikirin safe da yamma, da lokacin bacci.
    54. Yawan zikri yana ฦ™are mutun daga munafunci domin munafukai basa ambaton Allah da yawa.

    Misalin zikri,ู„ุงุงู„ู‡ ุงู„ุงุงู„ู„ู‡ ูˆุญุฏู‡ ู„ุง ุดุฑูŠูƒ ู„ู‡ ู„ู‡ ุงู„ู…ู„ูƒ ูˆู„ู‡ ุงู„ุญู…ุฏ ูˆู‡ูˆ ุนู„ู‰ ูƒู„ ุดูŠุก ู‚ุฏูŠุฑ
    duk wanda ya karanta wannan zikri ฦ™afa 100, da safe zai sami abubuwa guda biyar:
    Kamar ya ฦดanta bayi goma, sai lada 100, za a kankare masa zunubi 100, zai zame masa tsari daga sheษ—an a wannan rana har zuwa yamma,...    less
    • 5 people like this
  • Maishaq Muhammad
    Maishaq Muhammad
    Wai Mai Yasa Al’ummah Duk Da Irin Kiranye Kiranyen Da Malamai Keyi Akan Gyaran Zuciya Basaji Ba Sa Kuma Yi Sai Watan Ramadhana Yazo, Anan Ne Zakaga Jin Tsoron Ubangiji Amma Da Zarar Watan Ya Gabata Sai Kuma Akoma Tamtar Ba’ataba Jin Tsoron Ubangiji Ba?!
    March 31, 2021
    • 4 people like this
    • Maishaq Muhammad
      Idris Usman Gaskiya kam Allah yasa mudace
      • March 31, 2021
      • -
      • 1 likes this
      • -
      • Report
    • Maishaq Muhammad
      Maishaq Muhammad Aameen Mak Idris
      • March 31, 2021
      • -
      • Report
  • Maishaq Muhammad
    Maishaq Muhammad
    Assalamu Alaikum...
    Barkanmu Da Wayewar Garin Wannan Rana, Al’ummar Musulmi, Tareda Fatan Mun Wayi Gari Lafiya, Fatan Dinbin Alkhairi Agaremu Baki, Allah Yasadamu Da Alkhairan Dake Cikin Wannan Rana, Ya Karemu Daga Sharrin Dake Cikin Wannan Rana, Aameeen.
    March 31, 2021
    • Lawan Dalha, Rahmatu Lawan, and Bakandamiya like this.
  • Maishaq Muhammad
    Maishaq Muhammad liked Hauwa Dalha's post.
    March 30, 2021
    Hauwa Dalha shared Ummy Usman's blog.
    • 5 people like this
    • Maishaq Muhammad
      Maishaq Muhammad Masha Allah, Muna Godiya Sosai
      • March 30, 2021
      • -
      • Report
  • Maishaq Muhammad
    Maishaq Muhammad liked Mustapha musa abu Aisha's post.
    March 30, 2021
    Mustapha musa abu Aisha
    KARANTA SURATUL BAQARA A...  more
    Mustapha musa abu Aisha
    KARANTA SURATUL BAQARA A GIDA


    Manzon Allah ๏ทบ ya kwadaitar da mu akan yawaita karanta Suratul Baqara a gida, domin karanta musamman a gida akwai albarka ta musamman....  moreKARANTA SURATUL BAQARA A GIDA


    Manzon Allah ๏ทบ ya kwadaitar da mu akan yawaita karanta Suratul Baqara a gida, domin karanta musamman a gida akwai albarka ta musamman.

    Manzon Allah ๏ทบ yana cewa:-
    *(Ku riqa karanta Suratul Baqara, domin roฦ™on karanta albarka ne, rashin...    
    • Bakandamiya, Lawan Dalha, and Maishaq Muhammad like this.
  • Maishaq Muhammad
    Maishaq Muhammad commented on Abubakar Sulaiman II's photo.
    March 30, 2021
    Yadda Talauci Yake Bin Mutum Dagudun Bala'i A Mulkin Buhari ๐Ÿ˜‚๐Ÿ˜‚๐Ÿ˜‚๐Ÿ˜‚๐Ÿ˜‚
    • 6 people like this
    • Maishaq Muhammad
      Maishaq Muhammad Subhanallah
      • March 30, 2021
      • -
      • Report
  • Maishaq Muhammad
    Maishaq Muhammad liked Abubakar Sulaiman II's photo.
    March 30, 2021
    Yadda Talauci Yake Bin Mutum Dagudun Bala'i A Mulkin Buhari ๐Ÿ˜‚๐Ÿ˜‚๐Ÿ˜‚๐Ÿ˜‚๐Ÿ˜‚
    • 6 people like this
    • Maishaq Muhammad
      Maishaq Muhammad Subhanallah
      • March 30, 2021
      • -
      • Report
  • Maishaq Muhammad
    Maishaq Muhammad liked Mustapha musa abu Aisha's post.
    March 30, 2021
    Mustapha musa abu Aisha
    *MU KOYI IBADA*

    *Darasi Akan...  more*MU KOYI...  more
    Mustapha musa abu Aisha
    *MU KOYI IBADA*

    *Darasi Akan...  more*MU KOYI IBADA*

    *Darasi Akan Azumi*

    FITOWA TA BAKWAI-๐ŸŽต

    ABUBUWAN DA KE KARYA AZUMI

    *1-Jima’i:Akwai kaffara amma banda matar.Namiji ne kawai zai yi kaffarar* @Majmu’ul fatawa

    *2-Zuwan Jinin Haila*

    *3-Cin abinci da gangan*

    *4-Yin amai da gangan*

    *5-Zuwan jinin haihuwa*

    *6-Shan taba ko wiwi da rana dama ita taba haramun ce shanta ko ba da Azumi ba*

    *7-Allura a matsayin abinci ko qarin ruwa*

    *8-Yin qarya tana vata Azumi ba karyawa ba*

    *9-Cin duk wani abu mai Daukar sunan abinci da gangan*

    ABUBUWAN DA BA SA KARYA AZUMI

    *1-Kwana da janaba a jiki.Annabi ya kan wayi gari da janaba kuma yana mai azumi*

    *2-Kurkure ‘baki da shaqa ruwa da yin aswaki*

    *3-Sanya tozali da rana*
    @Fathul Bari

    *4-Sanya maganin ciwon ido*

    *5-Sanya maganin ciwon kunne*

    *6-Fitar maniyyi ta mafarki da rana*
    @Subulussalam

    *7-Yin qaho*
    @Bukhari

    *8-Rungumar mace da sumbatarta in ba ka da kaifin sha’awa*

    *9-Zuba ruwa mai sanyi a fuska ko a kai*

    *10-Dandana abinci amma a tofar bayan dandanawar*

    *11-Amai ba da gangan ba.*

    *12-Maganin da masu cutar ‘ASMA’ ke anfani da shi wato ( Inhaler ) lokacin azumi ba ya karya azumi*

    *13*Shaqa maganin mura*

    *14-Dibar jini a jikin mai azumi ba ya karya azumi*
    @Fatawas-siyam, Uthaymin

    *15-Cin abinci da mantuwa.[Allah ne ya ciyar da kai babu komi azuminka na nan]*

    *16-Yin asuwaki ko makilin da burushi*
    @Siyamu Ramadana na Jamil Zainu

    *17-Yin wanka a rafi*

    *18-Zuba ruwa a kai domin jin sanyi*

    *19-Yin allura a jiki da sunan Magani bata karya azumi*

    *20-Cire haqori ko cikesa ba ya karya azumi*
    @Munajjid 70 Questions on Fasting

    Idan mace tana da ciki sai ta ga jini ya zubo mata a gabanta,babu komai domin wannan ba jinin haila ba ne, azuminta yana nan bai lalace ba, ciwo ne ta nemi magani.

    Amma da a ce tana haila sai ta ga hailarta ta dauke bayan alfijir ya fito ba zata yi azumi ba.
    @Fatawas-siyam, Uthaymin

    SHAN MAGANIN DAUKEWAN JININ HAILA DOMIN MACE TA YI AZUMI

    Musulinci addini ne mai sauki baya kallafa ma mutum abin da bai iya wa, akwai hikimar Allah wajen yin hailar mace,Allah bai daura wa mace cewa ta sha wani magani domin jinin hailarta ya tsaya ba,amma da za ta sha wani magani domin hailarta ta tsaya babu komai kuma azuminta ya yi
    matuqar dai wannan jinin ya tsaya,da sharadin cewa wannan maganin da ta sha baya cutarwa.

    *Babban Malamin Hadisi Sheikh Muhammad Nasiruddeenil Albani ya ce babu laifi don mace ta sha magani don hailarta ta tsaya don ta yi azumi ko Hajji ba bu kome a gareta kuma azuminta ya yi*
    @Fatawas-siyam, Uthaymin

    *Shima Sheikh Mustafal Adawi ya ce babu komai azuminta ya yi indai wannan maganin ba zai cutar da ita ba kuma jinin zai dauke baki daya, amma da jinin zai dawo azuminta ya vace kuma sai ta rama wannan azumin*
    @Fatawa Sheikh Albani 232

    *Ya Allah ka isar da rayuwar mu watan Ramadhana muna imani da kyakkyawar...    less
    • 4 people like this
    • Maishaq Muhammad
      Maishaq Muhammad Allah Yayi Albarka Allah Yasa Mu Dace
      • March 30, 2021
      • -
      • Report
  • Maishaq Muhammad
    Maishaq Muhammad liked Mustapha musa abu Aisha's post.
    March 30, 2021
    Mustapha musa abu Aisha
    *_MA'ABUTA TAUHEEDI ALLAH YA HARAMTA MASU SHIGA WUTA_*

    Suwane ne ma'abuta Tauheedi??
    Ma'abuta...  more
    Mustapha musa abu Aisha
    *_MA'ABUTA TAUHEEDI ALLAH YA HARAMTA MASU SHIGA WUTA_*

    Suwane ne ma'abuta Tauheedi??
    Ma'abuta Tauheedi sune:-
    "Masu bautar...  more*_MA'ABUTA TAUHEEDI ALLAH YA HARAMTA MASU SHIGA WUTA_*

    Suwane ne ma'abuta Tauheedi??
    Ma'abuta Tauheedi sune:-
    "Masu bautar Allah shi kadai tare da Ikhlasy tare riko da tafarkin Manzon Allah SAW,Sannan basu Shirka da Allah ko kadan,sannan sun nisanci dukkan Bidi'a da Son Zuciya,sune wadan sukayi imani da Allah shi kadai a matsayinsa na ABIN BAUTA NA GASKIYA kuma sukayi Imani da SUNAYEN ALLAH DA SIFFONSA MADAUKA,sannan basu wuce gona da Iri acikin sunayen Allah da siffofinsa,sannan sune sukayi Imani da Allah A matsayinsa na RABBU,wato shi kadan yake da Hallita kuma ya mallaketa kuma yake gudanar da al'amarinta baki daya..............".

    Manzon Allah ๏ทบ yanà cewa:-
    *(Babu wani daga cikin mutane da zai Shaida babu abin bautawa na gaskiya sai Allah shi kadai,kuma Annabi Muhammad ๏ทบ Manzon Allah ne,yana mai gaskata hakan acikin zuciyarsa,face Allah ya haramta masa shiga wuta)*
    @ุตุญูŠุญ ุงู„ุจุฎุงุฑูŠ - ุฑู‚ู… ุ› (128)

    Mi ake nufi da Shaidawa babu abin Bautawa da gaskiya sai Allah;-
    *Yana nufi zuciyarka ta yarda hakan ta amince kuma ta gaskata hakan,sannan ka furta hakan da baki sannan ka bayyyana haka ta hanya yadawa tare da Ilimi hakan*.

    Daga Ubbata bn Samit ุฑุถูŠ ุงู„ู„ู‡ ุนู†ู‡ Yace,naji Manzon Allah ๏ทบ yana cewa:-
    *(Duk wanda ya Shaida babu abin bautawa na gaskiya sai Allah shi kadai,kuma Annabi Muhammad ๏ทบ Manzon Allah ne,Allah ya haramta masa wuta)*
    @ุตุญูŠุญ ู…ุณู„ู… - ุฑู‚ู… : (29)

    Manzon Allah ๏ทบ yanà cewa:-
    *(Lallai Allah ya haramtawa Wuta cin naman wanda yace LAA ILAHA ILLALLAHU kuma yana nufin fuskar Allah da fadar hakan)*
    @ู…ุชูู‚ ุนู„ูŠู‡ : (425-33)

    ุงู„ุดูŠุฎ ุงู„ุนู„ุงู…ุฉ ุฒูŠุฏ ุจู† ู…ุญู…ุฏ ุจู† ู‡ุงุฏูŠ ุงู„ู…ุฏุฎู„ูŠ ุฑุญู…ู‡ู ุงู„ู„ู‘ูฐู‡

    yana cewa;-
    Allah ya haramtawa wuta cin Naman ma'abuta TAUHEEDI,daga cikinsu àkwai wanda Allah ya haramta masa wuta gaba daya bazai taba shiga wutaba,sune masu imanin cikakke kuma masu ingantaccen tauheedi,wadan nan Allah ya haramta masu shiga wuta har abada,amma ma'abuta aikata manyan zunubai daga cikin ma'abuta TAUHEEDI kuma suka mutu basu tubaba,su wadan nan suna karkashin ganin dama ta Allah idan yaga dama ya gafarta masu ya shigar da su aljanna ba tare da wuta azaba ba,idan kuma yaga dama ya kama su da azaba daga baya ya shigar da su aljanna domin matsayinsu TAUHEEDIN da yake tare da...    less
    • 4 people like this
    • Maishaq Muhammad
      Maishaq Muhammad Allah Yasaka Da Alkhairi
      • March 30, 2021
      • -
      • Report
  • Maishaq Muhammad
    Maishaq Muhammad
    Assalamu Alaikum...
    Barkanmu Da Wannan Lokaci Tare Fatan Alkhairi Ga Daukacin Ma’abota Wannan Manhaja Ta Bakandamiya, Allah Yasa Mu Karashe Yunin Wannan Lokaci Cikin Aminchi!
    March 30, 2021
    • 7 people like this
    • Maishaq Muhammad
      Rahmatu Lawan Waalaikum salam. Barka dai barka dai, Mal. Maishaq
      • March 30, 2021
      • -
      • 1 likes this
      • -
      • Report
    • Maishaq Muhammad
      Mukhtar Musa Karami Abu Hisham Wa'alaikassalam Barka dai,fatan kana lafiya
      • March 31, 2021
      • -
      • 1 likes this
      • -
      • Report
  • Maishaq Muhammad
    Maishaq Muhammad liked Bakandamiya's blog entry.
    March 28, 2021
    Wa yake cin riba a hauhawar farashi, โ€˜yan kasuwa ko gwamnati?
    A ci gaba da kawo muku karon battar fasahar da marubuta ke yi a muhawarar da Bakandamiya ta shirya ta kuma ษ—auki nauyin aiwatarwa, a yau za ku ga yadda Hazaฦ™a Writers Association da Yobe Authors Forum suka ษ“arje guminsu tare da ruwan hujjoji a maudu&rsquo...
    • 7 people like this
    • Maishaq Muhammad
      Jibrin Adamu Rano Madallah da wannan manhaja. Har an tuno min yadda muka ษ“arje gumi.๐Ÿ˜
      • April 22, 2021
      • -
      • 1 likes this
      • -
      • Report
    • Maishaq Muhammad
      Bakandamiya Godiya muke Barrister!
      • April 22, 2021
      • -
      • 1 likes this
      • -
      • Report
    • Maishaq Muhammad
      Shu'aibu Ahmad Masha Allah
      Alah ya kara basira
      • May 3, 2021
      • -
      • 1 likes this
      • -
      • Report
  • Maishaq Muhammad
    Maishaq Muhammad liked Mustapha musa abu Aisha's post.
    March 16, 2021
    Mustapha musa abu Aisha
    #MUTANE SUN KASU KASO BIYAR 5 GAME DA LADAR SALLAR SU

    ุงู„ุนู„ู‘ูŽุงู…ุฉ ุงู„ุฅูู…ูŽุงู…ู ุงุจู’ู†ู ุงู„ู’ู‚ูŽูŠู‘ูู€ู€ู€ู€ู…ู ุฑูŽุญูู…ู€ู€ู€ู€ูŽู‡ู ุงู„ู„ู‡...  more
    Mustapha musa abu Aisha
    #MUTANE SUN KASU KASO BIYAR 5 GAME DA LADAR SALLAR SU

    ุงู„ุนู„ู‘ูŽุงู…ุฉ ุงู„ุฅูู…ูŽุงู…ู ุงุจู’ู†ู ุงู„ู’ู‚ูŽูŠู‘ูู€ู€ู€ู€ู…ู ุฑูŽุญูู…ู€ู€ู€ู€ูŽู‡ู ุงู„ู„ู‡ ุชุนุงู„ู‰ูฐ-:
    Yana...  more#MUTANE SUN KASU KASO BIYAR 5 GAME DA LADAR SALLAR SU

    ุงู„ุนู„ู‘ูŽุงู…ุฉ ุงู„ุฅูู…ูŽุงู…ู ุงุจู’ู†ู ุงู„ู’ู‚ูŽูŠู‘ูู€ู€ู€ู€ู…ู ุฑูŽุญูู…ู€ู€ู€ู€ูŽู‡ู ุงู„ู„ู‡ ุชุนุงู„ู‰ูฐ-:
    Yana cewa:
    "Mutane sun kasu kaso biyar 5 game da sallarsu da kuma matsayin sallarsu a wajan Allah:-

    1-Mai laifi wanda Allah zaiyi masa Uquba saboda sallarsa.

    Shine wanda baya cika sallarsa baya alwalar sallar ciakkiya kuma baya cika rukunan sallah baya cika wajiban sallar baya cika sharuddanta,yana yin sallar ne yanda yaga dama,sallarsa ta sabama irin Sallar Manzon Allah s.a.w, to mai irin wannan sallah Allah zaiyi masa uquba saboda sallarsa.

    2-Wanda Allah zaiyi masa Hisabi akan sallarsa.

    Shine wanda zaiyi sallah yazo da ita da rukunnanta da wajibanta da Sharuddanta,sai dai tun daga lokacin da aka kabbara sallar bai san ake cikiba har zuwa sallama,saboda zuciyarsa ta shiga tunani da shagala da tuniya ya manta ma sallah yake,da zaka tambayesa wani sura aka karanta bazai iya tunawa ba saboda zuciyarsa da tunaninsa basu cikin sallah,mai irin wannan sallah shine Allah zaiyi masa Hisabi akan sallarsa.

    3-Akwai wanda Sallarsa take kankare masa laifukansa.

    Shine wanda zai zo da sallarsa cikakkiya da rukunnanta da wajibanta da Sharuddanta cikakku,amma tun daga lokacin da ya shiga cikin sallar to yana cikin sauri da gaggawar yaga angama sallar,shaidhaninsa yana so ya karkatar da zuciyarsa amma yana kokarin yaki da zuciyarsa da shaidhan yaga ya maidao da hankalinsa gaba da akan sallarsa,mai irin wannan sallah shine Allah yake kankare masa laifunsa na tunanin da yake da saurin da yake acikin sallarsa,saboda jihadin da yayi na kokarin maido da zuciyarsa da tunaninsa cikin sallar.

    4-Wanda yake dacewa da samun ladar sallarsa mai girma.

    Shine wanda ya zo da sallarsa cikakkiya ta wajan rukunnanta da sharuddanta da wajibanta,da mustahabbanta tare da khushu'i da na zuciya dana gabbai ba tare da wani tunanin duniya ba acikin sallarsaba,to mai irin wannan sallah shine wanda Allah yake bashi ladar cikakkiyar sallarsa.

    5-Wanda sallarsa take sanya ya sami kusanci da ita awajan Allah.

    Wannan shine matsayin mai sallah mafi daukaka,shine wanda zaizo da sallarsa,cikakkiya ta wajan rukunnanta da sharuddanta da wajibanta,da mustahabbanta tare da khushu'i da na zuciya dana gabbai ba tare da wani tunanin duniya ba acikin sallarsaba tare da halarto Allah a zuciyarsa wato yana ganine na musamman da Allah zuciyarsa tana mai cike da tuna Allah da halartosa acikin sallarsa.
    Dukkan wanda yazo da sallah wadda take dauke da sharudda da rukunnnai da wajibai da mustahabbai da khushu'i da cikakku tare da halarto Allah da tuna Allah da gani dashi kadai acikin sallarsa,kuma Allah yana kallonsa to hakika ya sami matsayi mafi daukaka daga cikin matsayin masu sallah,shine ya sami kusancin Allah ta dalilin wannan sallah...    less
    • 7 people like this
    • Maishaq Muhammad
      Amina Muhammad Ameen ya rabbi
      • March 16, 2021
      • -
      • Report
  • Maishaq Muhammad
    Maishaq Muhammad liked Hafsat Moh'd Arabi's post.
    March 16, 2021
    Hafsat Moh'd Arabi
    A Koda Yaushe Allah Zai Mana...๐Ÿคฒ Allah Kada fa Mana๐Ÿคฒ
    • 8 people like this
    • Maishaq Muhammad
      Rahmatu Lawan Amin Ya Allah
      • March 16, 2021
      • -
      • 1 likes this
      • -
      • Report
    • Maishaq Muhammad
      Zaharadden Nasir A kodayaushe Allah zai yi mana... Allah ka dafa mana
      • March 16, 2021
      • -
      • 3 like this
      • -
      • Report
    • Maishaq Muhammad
      Hafsat Moh'd Arabi Ameen ya Allah
      • March 16, 2021
      • -
      • Report
    • Maishaq Muhammad
      Mukhtar Musa Karami Abu Hisham Amin
      • March 16, 2021
      • -
      • 1 likes this
      • -
      • Report
View More
Loading ...

About

Personal Information

  • Sunan Farko Maishaq Muhammad
  • Jinsi Namiji
  • Ranar Haihuwa April 4, 1994
  • Takaitaccen Bayani Ma'aboci karance karance ne domin karin ilmi da kaifin basira, Ma'abicin tafiye tafiye ne domin kara bude idabuwa cikin zamantakewa, Ma'abocin gudun cutarwa ne kuma Mai Rajin kare hakkin marayu, Mata da Yara duka. Bakomai bane kazama daidai haka ma bakomai bane na rashin daidai ka'iya zama daidai.

Contact Address

  • Sunan Gari Kaduna
  • Karamar Hukuma Kaduna North
  • Sunar Jaha Kaduna
  • Sunar Kasa Nigeria
© 2022 Bakandamiya About Terms Privacy Subscription Earn Money Advertise Contact
  • Facebook
  • Twitter
  • Linkedin
  • Youtube
  • Pinterest
  • Instagram