fiddausi sani
*INTELLIGENT* *WRITTER'S* *ASOCIATION*
( on ward together )
*ASALINA*
*Story* *and* *written*
By
*FIDDAUSI* *SANI*
( damsel feedorh )
🅿️:6️⃣5️⃣
*INa* *Masu* *bibiyar* *labaran* *shahararriyar marubuciyar nan wato *FATIMA* *EYMAN* , *wacce* *ta* *saba* *nishadan* *tar* *daku* *hadi* *da* *fadakarwa* a littafanta irin su 👇
*MATAR* *YAYA* *NA*
*UNCLE* *SADIK*
*HURTFUL* *HEART*
*KAUNA*
*da* *dai* *sauransu* . *ALHMDULLAH*
*this* *is* *the* *last* *free* *page* *of* *the* *book* *AFTER WEDLOCK* 🥰
*GA MASU SAN CIGABAN LITTAFIN BAYAN AURE ZASU IYA BIYAN NAIRA 300 TA WANNAN ACCOUNT DIN 👉🏼 3139940656 {SULEIMAN FATIMA MUHAMMAD} FIRST BANK*
*KO KUMA A TURA KATIN WAYA {MTN} NA 300 ZUWA WANNAN NUMBER {08103810398},*
_please If u make ur payment, kindly screenshot and send ur evidence through my WhatsApp digit 👉🏻{08103810398}_
_Patronize and read with full of happiness 💓 Real~Teemarh
,,,,,,, Bata ankara ba sedai taji wata mata da take kusa da ita tace "baiwar Allah ki sauka mun iso, fita sukayi a cikin tashan nan tafara raba ido ta rasa inda zata dosa wani runfa ta samu ta zauna, tana tunanin inda zata samu wurin kwanciya
tana zaune sega wata 'yar tsohuwa tazo da kullin kayanta ga alama dai akwai abunda take sedawa, saboda yanda taga ta zauna tana ta lissafin kudi, seda taga ma tsaf ta kulle a habar zani, tashi tayi da nufin tafiya da sauri Umma tace "bahba dan Allah tambaya nake, juyowa tsohuwar tayi ga alama se yanzu ne tagan ta a wurin, tsaya wa tayi tace "inajinki "taimakona, zakiyi da wurin kwana a hanya nake gashi dare yayimin, zuwa gobe se na karasa inda zantafi, shiru tsohuwar tayi kamar me tunani zuwa can tace ba'anan nake ba nima ke kuwa yarnan me ya kaiki tafiyar dare gaki da danyen goyo" ehhh darene yayimun Umma tabata amsa "to kinga nima ba'anan cikin garin kano nake ba ina Gezawa ne, idan zaki bini ne to mutafi, babu musu Umma tagyara goyon ta, ta dauki kayanta tabi tsohuwar
Motar da ke zuwa Gezawa suka shiga, anyi tafiya me dan nisa tukuna suka iso, Umma zata biya kudi tsohuwar ta dakatar da ita, bakin zanen ta ta kwance ta bada kudin motar, Napep ta tarar musu ta fada mishi unguwar da zasu tafi.
Abakin wani gida suka sauka gidan a rufe yake, seda ta bude sa jamlock tukuna suka shiga, tsaf suka same gidan da alama tsohuwar tana da tsafta, tabarma ta daukowa Umma tace ta zauna ta baiwa 'yarta no-no taga se mutsu mutsu take babu musu Umma ta zauna, kwance Humaira tayi, ta rage mata kayan da suke jikinta kasancewar lokacin zafi ne
tana zaune ta kawo mata ruwa amsa tayi tare da godiya, kujera tsohuwar ta dauko ta zauna, ganin da tayi Humaira na kuka kuma Umma taki bata No-no ne yasaka ta cewa "kekuwa kibata abincinta tasha mana shiru Umma tayi daga bisani tace "Nonon nawane baida lafiya likita ya hana nabata shi "ikon Allah to me kike bata? Jakar da ke kusa da ita ta janyo, madarar tafara fitar wa tace wannan nake bata "to shine kuma kika barta tana kuka, maza kibata tasha to "ehhh dama se an dama da ruwan zafi umma tabata amsa, tashi tsohuwar tayi tafara kunna wuta
Ruwan zafi ta dora a babban tukunya, seda yatafasa tace "to kema yakamata kitashi kiyi wanka naga kamar sabon haihuwa ne, tashi umma tayi kuwa tshowar da kanta yakaimata ruwa bayi harda towel tabata ita a tunanin ta wankan jego Umma zatayi, seda umma tafara damawa Humaira madara, tukuna tabaiwa tsohuwar tace "Bahba gashi kibata kafin nafito wanka.
Washe gari tunda asuba Bahba tasake dora mata ruwan zafi, seda sukayi wanka, ta damawa Humaira madara, sega tuwo Bahba ta shigo dashi da alama makota ta siyoshi, ajewa tayi gaban Umma tace "kisamu kici abincin nan naga mai jego tafison tuwo shiyasa na siyo miki godiya sosai Umma tayi mata, batare da kyankyami ba taci tuwonta kuwa, tana gamawa ta goya Humaira, ta dauki kayanta akan zata tafi "ke kuwa 'yarnan da wannn sammako kamar ana korarki ko nesa ne inda zaki tafi "ehhh to yanzu dai bansan inda zantafi ba amma neman haya zanje ko zansamu, kallonta Bahba tayi tace "haya fa kikace, ba gun 'yan uwanki zakitafi ba, dawowa Umma tayi ta zauna tace "Bahba ni da kike gani banda kowa se Allah da kuma wannan 'yar da yabani, ni 'yar asalin maiduguri ce a hare-haren boko haram suka kashe kowa nawa harda mijina, Allah ne ya kubutar dani da 'yata shiyasa naga gara nabar garin to me zanyi babu uwa babu uba, kuma shima mijin sun kashe, cikeda tausayi Bahba tace "Allah sarki Allah ya gafarta musu yamuna maganin wayannan yan boko haram, ke kuwa yarnan ai tun farko yakamata ki fadamin haka yanzu idan kika kama haya Kinada kudin da zaki rika biyane, kinga indai zaki iya zama anan dukda kauyene ke kuma da alama kamar bakisaba da wahala ba, to babu matsala ga dakinan zanbaki kyauta dama 'dana guda ne kuma a cikin garin kano yake sana'ar faci, nikuma nakan shiga kano tallan maganin daji jiya ma da kika ganni daga can nake, kinga idan zantafi sedai na rufe gida idan zaki zauna ai babu matsala, saboda gaskiya na tausaya miki rashin iyaye da kuma miji ba karamin abu bane, ga 'yar jinjira kuma, cikeda jin dadi Umma tace "na gode sosai Bahba Allah yasaka da Alkhairi "ay babu komai yiwa kaine, tafi ki ajiye kayanki.
Wannan shine dalilin zaman Umma a kano kauyen Gizawa, inda tayi rayuwa yau dadi gobe akasin hakan ka sancewar Bahba ba wani karfine da ita ba, se ya kasance abincima ba ko yaushe ta ke samu ba hakanne yasaka ta fara neman wanka kau, saboda tarufawa kanta da 'yarta asiri, cikin dan lokaci Umma tafara canjawa, tafara hadewa da yangarin sam bazakace tayi wani karatun Boko ba, itama bata nuna tayi karatun ba, haka take fadi tashi gashi Humaira harta shiga wata na 7 alokacinne madarar da takesha ya kare hankalin Umma ya tashi saboda batada kudin siya idanma tana dashi to a ina zata siya tasan dai a Gizawa baza'a samu madarar ba, dole tafara sayen koko tana baiwa Humaira, cikin sa'a kuwa Humaira tafara shan koko hakan yayiwa Umma dadi, tana matukar son Humaira ko yaushe tana tare da ita sam bata iya nisa da ita
suna wannan rayuwar ne ciwo yakama Bahba, zazzabi kamar wasa, segashi ta kwanta ya kasance bata ma fita, hankalin Umma ya tashi sosai, gashi "dan da take cewa shi kadaine da ita tunda tazo gidan bai zo ba, ranar dai da taga jikin Bahba ya tsanan ta, haka ta zauna ta nata kuka, duk tausayin tsohuwar da kuma tunanin mako marta idan tarasu takeyi, dakyar Bahba tayi magana cikin magagin ciwo tace "Habiba kidena kuka ciwo ai ba mutu bane, ni tunani na idan na mutu yanzu wane hali zaki shiga da 'yar marainiyar Allah, hakan yasakani na yanke hukunci sedai bansani ba ko nayi shishigi a cikin rayuwar ki, baki da kowa kuma ina tsoron, ki salwantar da rayuwarki tunda kika zauna gidan nan na fahimci kedin mutuniyar kirki ce, kina girma mani kamar nice na haifeki, dan Allah Habiba ki amince ki auri 'dana Ahmad na tabbata ze kula dake kuma shine kawai nakeda yakini akanshi, shiru Umma tayi ita kam taya zata auri mutumin da ko mahaifiyar shi baidamu da ita ba, ace wata 7 baka zo ka duba halin da take ciki ba, kuma kuna gari daya, gashi ita bata bar gida da niyar tayi aure ba ta so idan wani lokaci tayi ta waiwaye danginga amma auren ta anan yana nufin zaman ta na har abada, to idan kuma shi Ahmad din yace baya sonta fa, katsemata tunani Bahba tayi da fadin "nayi miki shishigi ko "aa Bahba ke din uwa ce me neman rufawa 'yarta asiri na amince zan aureshi matukar shima ya yarda, duk da Bahba tana cikin ciwo amma zaka fahimci taji dadin amincewar Umma, adress din Ahmad tabata a kano tace ta tafi ta sanar da shi cewa bata da lafiya, haka Umma ta shirya ta tafi, bata sha wahala ba tagane Ahmad, faada mishi abunda ke faruwa tayi, cikin hanzari yahada kayanshin a tare da ita suka nufo Gezawa
hankalin shi yayi matukar tashi ganin yanda Bahba ke jinya, kuka yayi sosai yana fadin "tayi hakuri rashin zuwan da baiyiba cikin lokaci "babu komai Ahmad nasan kaidin yaro ne me biyayya saboda haka nakeso ka auri wanann yarinyar, da sauri ya kalli Umma kasa tayi da kanta, baba tace "Ahmad kaga wannan 'yar da take bayanta marainiya ce ankashe mahaifinta, itace wacce ta kula dani lokacin da bakanan, Ahmad ban amince ka saki Habiba ba ko bayan Raina kuma wannan gidan ko mutuwa nayi bakai ne na barwa wa, nabaiwa Marainiyar Allah Humaira, saboda basu da kowa se Allah kuma bansan me gaba zata haifar ba maza Bakuda tabbas duk da nasan kaidin bazakayi haka ba, karike Humaira kamar yanda zaka rike yar cikinka Ahmad kar kabari ta fahimci bakaine mahaifin ta ba dan Allah "insha Allah Inna zankula yanzu bari mutafi asibiti, kin amincewa ta yakaita a asibiti babu yanda basu yi da ita ba amma taki kwanan Ahmad biyu da zuwa Bahba tace ga garinku ne Umma tayi kuka sosai kamar ranta zefita, gara Ahmad shi namiji ne yayi karfin hali, bayan sadakar bakwai aka daura auren Umma da Ahmad, a cikin gidan yabarta, sosai Umma take kewar Bahba gashi bawani sabo ne tsakanin ta da Ahmad ba sedai ta fahimci yanason Humaira, duk sati yake zuwa Gezawa ganinsu kuma duk zezo se ya siyowa Humaira kayan wasa sosai yake janta a jikinshi wanann kulawar da yake bata ne yasaka Umma saurin sakewa da shi saboda tanason duk wanda keson Humaira
Rayuwar auren su se muce rayuwa ce ta girmama juna kawai bawai soyayya ba, shekararsu daya da aure Ahmad yanemi su koma cikin garin kano da zama tunda acan yake kasuwanci hakan zefi masa sauki, babu musu Umma ta amince, lokacin Humaira ta kusa shekara 2 tafiya take ko ina da kafarta, tasaba da Abba sosai, komai Abba shine kawai sunan da ta iya fada se dai tayita gwalamniya irin na yara, komawar su kano ne suka fara gina rayuwar auren su saboda sun yarda cewa a yanzu babu mafita sun zama abu daya, cikin ikon Allah Umma ta samu ciki,,sosai Abba yake murna da samuwar cikin Umma yana kokari sosai wurin kula dasu, har Allah ya sauketa lafiya lokacin Humaira shekarar ta 3 tayi wayo sosai gata yarinya mai kyau tana da saurin shiga rai, mace Umma ta haifa taci sunan Fadila, Sam Humairq bata bari ataba kanwarta komai zatace Fadila, zama suke cikin kwanciyar hankali, suke kulada ' yayansu, har Fadila tafara wayo, sedai Umma tafi nuna soyayyar ta akan Humaira hakan yasamo asaline saboda tausayin ta da takeyi, sosai Abba yake mata fada akan hakan, duk da bawai tana nunawa a fili bane sedai ya na nuna mata dukansu yayan tane, suna haka, kwatsam sega maganar karin auren Abba Umma ta shiga damuwa ganin a gidan haya suke zaune se ta bashi shawarar Kawai yasiyar da gidan Gezawa se yazo nan kano ko gida me daki 2 ne yasiya, sam Abba bai amince da hakan ba, cewa yayi gida na Humaira ne saboda haka basu da wanann hurumin "haba Abban Humaira yanzu abun Humaira ba namu bane ai ba cewa nayi ka dauka ba kamardai musaya ne, se mu zauna amma haya har gida biyu ga mutum mai karamin karfi ai akwai wuya, da wanann shawarar na Umma aka siyar da gidan suka siye wani a kano
tun kafin akawo Furera Umma taji labarin halinta, bazawara ce kuma mugun ha line yarabata da mijinta, gashi ance makirar mace ce, haka Umma tamika lamuranta ga Allah taciga ba da rainon yaranta, zuwan zuwaira shine yafara sauya komai a gidan sam Abba yafara janye kulawarsa saga iyalinshi komai dai Furera, rayuwar kunci tafara wa su Umma lokacin da Furera ta haifi Faruk, sewani rawar jiki Abba yake wai ya samu maitemakon shi dama ya mace sedai ka wahala da ita
#Vote and follow me on wattpad@damselfeedo
Its ur feedorh💘