• Contrast
    • Font
    • A
  • Sign In
  • Sign Up
    Loading ...
View All Updates Mark All Read
Bakandamiya
  • Shafin Farko
  • Mambobi
  • Zauruka
    • Browse Groups
  • Tambayoyi
  • Ra'ayoyi
    • Browse Polls
  • Makalu
    • Browse Entries
  • Bidiyoyi
    • Browse Videos
  • Sautuka
    • Nemo Sautuka
  • Hotuna
    • Browse Albums
    • Browse Photos
  • More
    • Kasuwa
      • Stores Home
      • Browse Stores
      • Browse Locations
      • Products Home
      • Browse Products
      • Products Pinboard
      • Categories
      • Browse Reviews
      • Wishlists
    • Sana'o'i
      • Browse Listings
    • Sanarwa
      • Bukukuwa Masu Zuwa
      • Past Events
  • Updates
  • About
  • Abokai(28)
  • Zauruka(1)

Updates

About

Personal Information

  • Suna Muhammad
  • Sunan Mahaifi Karim
  • Jinsi Na miji
  • Ranar Haihuwa May 5, 1997
  • Takaitaccen Bayani Allah Is My LORD
    Quran Is My Guide
    I Love Prophet Muhammad (S A W)

Contact Address

  • Sunar Unguwa kaduna [map]
  • Sunan Gari Kaduna
  • Karamar Hukuma Kaduna North
  • Jaha Kaduna
  • Kasa Nigeria

Abokai

  • Bakandamiya GORON JUMMAA MATAR DA BA TA DA AURE ZA TA IYA SANYA TURARE TA FITA UNGUWA? Tambaya: Assalam malam muna san karin bayani akansa turare gamata sufita, wani malami yace wadda ba matar aure ba zata iya sawa? Amsa: Wa'alaikum assalam, To 'yar'uwa ya HARAMTA ga mace Baliga ta sanya turare, ta fita unguwaa, saboda fadin Annabi S.A.W : "Duk matar da ta sanya turare, ta wuce ta wani majalisi, to ta zama mazinaciya, kamar yadda Abu-dawud ya rawaito. A wani hadisin kuma yana cewa: "Duk matar da ta sanya turare, kar ta halarci sallar Isha tare da mu. Nassoshin da suka gabata suna haramta sanya turare ga mace balagaggiya idan za ta fita, kuma ba su bambance tsakanin matar aure ba da budurwa ko bazawara, wannan sai ya nuna gamewarsu ga dukkan mata wadanda sharia ta hau kansu, tun da ba'a samu abin da ya kebance wasu nau'i ba, sannan kuma an haramta sanya turaren ne: saboda yana kaiwa zuwa tada sha'awar Maza, wannan kuma baya bambanta tsakanin matar aure da wacce ba ta yi ba Amma za ta iya sanyawa ta zauna a gida mijinta ya ji kamshi, in ta yi hakan za ta samu lada, haka ma budurwa, za ta iya sanyawa a tsakanin 'yan'uwanta mata, ko gaban muharramanta wadanda ta san ba za su yi sha'awarta ba Allah ne mafi sani Amsawa: DR. JAMILU YUSUF ZAREWA 31/03/2016
  • Lawan Dalha Ya Allah Ka sada mu da alkhairan da ke cikin wannan rana; ka tsare mu daga sharri duniya da lahira. #JummaaMubarak
  • Ummyter Abdallah Madam din Dana kewa aiki jiya ta aikeni na sayo mata semo 2kg,danaje shagon sai na tarar sai 1 kg,so na dawo ban sayo ba shine tace min ni Wawa ne bana amfani da hankalina na sayo 1kg guda biyu ya zama 2kg Kennan idan an hada,na bata hakuri dai ta hakura,yau kuma tace na sayo mata slippers number 8,danaje babu sai lamba 4 shine na sayo lamba 4 guda biyu,na kawo batace komai ba Naga tana hada mini kayana cikin jaka,shine nake tambaya ko wanki zatayimin koko daki zata canjamin🤪🤪🤪
  • Amrah Auwal *KU DUBE MU!* Amrah Mashi Nagarta Writers Association *'KU DUBE MU'* Wannan kalma ce da ta zama nanatau ga dan Nigeria a yau, ta zama mafarkansa da yake fatan cikarsu a duniyarsu. Rayuwarmu a dunkule take wajen hasko mana ababen da suke zama barazana ga shakar iskan da muke kyauta. Fargaba ta zama zananniyar shimfidar da ke kewaye da zukatanmu. Yaushe ne *ZA A DUBE MU?* Yaushe ne wannan tsoron zai tsere daga gare mu? Adadin hargitsattsun layukan da ke kara rikicewa su ne ke sare mana gwuiwa a kan sa ran da muke da shi. *KU DUBE MU!* Jinin bil Adama a Nigeria, ya zama tamkar jinin kaza ko zakara da ke fita a kowanne lokaci, ba tare da nadama ko da na sani ba, sai ma farin ciki ga masu ita, domin kuwa idan ba su ci ba a bakinsu, za su siyar su samu kudi! *KU DUBE MU!* Anya kuwa yadda ake haike wa matayenmu ba zai nemi rinjayar adadin ma'auratan da suke raya sunna ba? Ba fata nake ba. *KU DUBE MU!* Abincin cinmu tsada! Ruwan shanmu tsada! Suturar da za mu suturta jikinmu tsada! *KU DUBE MU!* Tafiya a mota ta zame mana dole, sai dai a kasarmu ta Nigeria tana neman gagararmu. Komai girman uzurin mutum a wasu lokutan dole ya jingine su domin ci gaban numfashinshi. *KU DUBE MU!* Mutum zaune a cikin gidanshi, yana tsaka da walwala da iyalinshi masu garkuwa da mutane za su shiga, su ruguza nishadinshi, su rusa walwala da annashuwarshi. *KU DUBE MU!* Ilmi yana neman gagararmu. Muna ji muna gani 'yan ta'adda suna neman nakasta mana zukata. Suna neman kawo tsaiko ga wannan ilmin da ya zama fitilarmu *KU DUBE MU!* Cin hanci da rashawa na dad'a samun muhallin zama a tsakanin 'ya'yan Nigeria. Inda mai kakkarfan laifi zai cika aljihun mahukunta da wasu 'yan silalla, su sake shi, ya koma ya ci gaba da aikata wancan laifin ba tare da nadama ba. *KU DUBE MU!* Muhalli na neman gagararmu. Mutum da gidanshi amma 'yan ta'adda za su hana su kwanciyar hankali, dole su bar wurin su koma inda yake da kwanciyar hankali. Su zauna a ina? Babu! A karshe kila sai dai bara. Rayuwa ta gurbata. *KU DUBE MU!* Nomar da muka gada tun iyaye da kakanni muna ji muna gani ta fi karfinmu. An tada mu daga gonakinmu. Idan mun fito a karkashe mu. Mun hakura mun rungumi kaddararmu. Ba dole abinci ya tsadance ba? *KU DUBE MU!* Shugabanni; Sarakunanmu, Attajiranmu, 'Yan kasuwanmu, 'Yan siyasarmu, Da duk wani mai fad'a a ji a fadin kasarmu ta NIGERIA, ina mai rokonku da ku dubi girman Allah KU DUBE MU. KU DUBE MU! KU DUBE MU! KU DUBE MU! ©️Princess Amrah
  • Mukhtar Musa Karami Abu Hisham Lokacin taron bada kyautukan gasar muhawarar Bakandamiya ,daga wanne gari zaka zo gurin taron?
  • faridat sweery 😂😂😂😂 Da haka abun ya zo.🏃🏾‍♀️🏃🏾‍♀️🤔
  • Haupha123 Tambaya. Shin ya zan rubuta kalmar .. Nagode ko Na gode ? Cikinsu da wane zan amfani ? Na gode. Nagode.
  • Maryam Haruna A rayuwata babu abin da nake so kamar kallon finafinai na tsoro da firgici hakan na min daɗi sosai wanda hakan yasa ko kallo zan yi bana kallon wanda na san babu wani abu da zai firgita mutane. Ko a makaranta abokan karatuna duk sun san wannan hali nawa,wani lokaci su kan bani shawara a kan in bari kada wani abu ya faru da ni amma da rana ɗaya ban taɓa sauraronsu ba tunanina ma yanda zan sa musu son fara kallon irin finafinan da nike yi ƙila hakan zai sa su fahimci abin da nake nufi da son waɗan nan abubuwan. Mu uku muke ɗakinmu na makaranta,kullum cikin hana ƴan ɗakinmu bacci da hayaniya in Ina kallo. Sun yi duk yanda zasu yi don hanani wannan ɗabi'ar amma hakan ya faskara,don bani da lokacin da nake jin daɗin kallon fim ɗin tsoro sai sha biyu na dare. Ashe ƙaddara ce ke bibiyata ban sani ba. Wata rana daga makaranta aka kai mu asibitin mahaukata wacce ke bayan gari kusa da maƙabarta. Na ji daɗi sosai don wasu finafinai da nike kallo yawanci a asibitin mahaukata ake bada tsoro duk tunanina tunda mun zo hakan zata faru ga waɗan da muka zo tare don ni bana saka kaina saboda ni na san na saba kallo to tsoron mi zan ji kuma. Ranar da ba zan manta da ita ba ita ce: bayan satinmu guda a asibitin ranar ina aikin dare sai na dinga jin kamar ana kuka sannan ana jan wani abu kamar ƙarfe cikin wani ɗaki da ke kusa da inda nake zaune. Wata mata ce ciki wacce tun da muka zo asibitin magani ko abinci kawai ke sa a buɗe ɗakin saboda yanda take duk wanda ya shiga ɗakin ƙoƙarin kashe shi take yi hakan yasa aka daina zuwa wajenta sai dole. Da farko na share saboda na san matar da ke ciki zata iya yin komai duba da yanda ciwonta yake amma kuma sai na ji abubuwan sai ƙaruwa suke yi,wata zuciya na cewa na duba wani gefen na gargaɗina a kan kada na je. Da dai na ji abin ya wuce tunanina ƙarar sai damuwata take yi hakan yasa kawai na tashi don zuwa ganin menene. Ina tashi sai wutar ɗakin ta dinga rawa kamar zata ɗauke. Ban damu ba na kunna fitilar wayata don in gani da kyau. Tura ƙofar ɗakin na faɗa ba tare da jiran wani abu ba,abin da na gani ne ya kusan sani sumewa. Wata halitta ce kusa da matar nan tana mata wani abu da na kasa gane meye matar dai kwance take kamar babu rai tare da ita wannan halittar sai zuƙar jinin jikinta dake ta malala ƙasa kamar ruwa . Hakan da na gani ya mugun tsoratani har ban san na saki wayata ba ashe dai duk rashin ganin tsoron da nake cewa bana shaci daɗi ne don ban gani a zahiri bane, ƙarar faɗuwar wayar yasa wannan halittar ta juyo inda nake cikin sakan ɗin da bai wuce goma ba na ƙare mata kallo. Ƙaton kai ne da ita kamar ƙwllo,wuya kuma ba kauri sai kace mariƙar lema. Ido guda gareta kuma a tsakiyar kai yake, ƙafafuwanta sun kusan shida ga wani gashi da ya rufe mata jiki wanda ya ƙara maidata abin tsoro. Ganin ta juyo inda nake yasa da sauri na zabura da gudu zan bar ɗakin ai kafin ƙyaftawar ido na ga ta kusa zuwa inda nake ban yi ƙasa a guiwa ba na ƙara azama wajen gudun da nake son yi. Ita ma kokarinta ta zo inda nake don lahanta rayuwata na yi gudu sosai kaɗan ya rage in buɗe ƙofar fita baƙi ɗaya sai kawai na ga kare bakin ƙofar gashi ya buɗe baki da alama jira yake na ƙaraso wajen shima ya illatani. Ganin haka na yi shahada tare da canja waje zuwa makewayin dake ɗakin sai dai me kafin in kai na hango wani mutum mai mugun tsawon da duk iya ganina na kasa ganin ƙarshensa,gashi kayan jikinsa baƙi wuluƙ da dai na rasa yanda zan yi kawai sai na rufe idona ina jiran mai faruwa ta faru. Ban san me ya faru ba sai dai na buɗe ido na ganeni kwance saman gado an ɗaureni da igiyoyi a yanda na ji ana magana wai sati na guda kenan da haukacewa kuma duka nake yi don haka aka ɗaureni yanzu haka mafita nake nema yanda zan faɗa musu cewar ba hauka nake ba.
  • Muhammad Sulaiman
  • Zaharadden Nasir Allah ka bamu lafiya. Marasa lafiya na gida da na asibiti, su ma Allah Ka basu lafiya
Previous
Next

Zauruka

  • INSIDE AREWA WRITERS
    s
    KUNGIYAR NAZARIN HARSHEN HAUSA
Previous
Next
© 2021 Bakandamiya  -  About Us  -  Terms  -  Privacy  -  Advertise  -  Support  -  Stock Photos  -  Contact Us  -  Mobile Apps
  • Facebook
  • Twitter
  • Linkedin
  • Youtube
  • Pinterest
  • Instagram
Create New Content
  • Kasuwa
Add Link