• Contrast
    • Font
    • A
  • Sign In
  • Sign Up
    Loading ...
View All Updates Mark All Read
Bakandamiya
  • Shafin Farko
  • Mambobi
  • Zauruka
    • Browse Groups
  • Tambayoyi
  • Ra'ayoyi
    • Browse Polls
  • Makalu
    • Browse Entries
  • Bidiyoyi
    • Browse Videos
  • Sautuka
    • Nemo Sautuka
  • Hotuna
    • Browse Albums
    • Browse Photos
  • More
    • Kasuwa
      • Stores Home
      • Browse Stores
      • Browse Locations
      • Products Home
      • Browse Products
      • Products Pinboard
      • Categories
      • Browse Reviews
      • Wishlists
    • Sana'o'i
      • Browse Listings
    • Sanarwa
      • Bukukuwa Masu Zuwa
      • Past Events
  • Updates
  • About
  • Abokai(10)

Updates

About

Personal Information

  • Suna Musa Baba
  • Sunan Mahaifi Ismail
  • Jinsi Na miji
  • Ranar Haihuwa March 1, 1981
  • Takaitaccen Bayani nide suna na Musa baba Ismail da Minna Niger State

Contact Address

  • Sunan Gari Minna
  • Karamar Hukuma chanchaga
  • Jaha Niger State
  • Kasa Nigeria

Abokai

  • Rahmatu Lawan Barkanmu da Jumma'a 'yanuwa. Allah Ya sada mu da albarkatun da ke cikinta!
  • Ummyter Abdallah Madam din Dana kewa aiki jiya ta aikeni na sayo mata semo 2kg,danaje shagon sai na tarar sai 1 kg,so na dawo ban sayo ba shine tace min ni Wawa ne bana amfani da hankalina na sayo 1kg guda biyu ya zama 2kg Kennan idan an hada,na bata hakuri dai ta hakura,yau kuma tace na sayo mata slippers number 8,danaje babu sai lamba 4 shine na sayo lamba 4 guda biyu,na kawo batace komai ba Naga tana hada mini kayana cikin jaka,shine nake tambaya ko wanki zatayimin koko daki zata canjamin🤪🤪🤪
  • Rufaida Umar Ku je marubuta group kar garaɓasa ta wuce ku!
  • Amrah Auwal 'Yancin Kai! Naija@60 By Princess Amrah NWA Da Me Za Mu Ji? Cin hanci da rashawa wanda ya zama tamkar ruwan shan dan Nigeria? Fyade da ake wa iyalanmu ba manya ba kananan yara? Rashin tsaro na wannan kasar tamu da ya zama makasar da damar al'ummarmu? Masu garkuwa da mutane da suka hana mu sakat a wannan kasar tamu ta Nigeria? Yan fashi da makami da ke zubar da jinin musulmi a kowacce dakika? Rashin darajta al'ummar musulmi da addinin musulunci baki daya? Ilimi da ke neman gagarar dan talaka? Tsadar abincin cinmu na yau da kullum? Ko kuwa tsadar man fetur? Da wannan ne zan yi murnar cikar shekara sittin da samun yancin kan Nigeria? A ina yancin yake? Nigeria da yanci ya'yan cikinta babu yanci? Nigeria da yanci abincin ci ya gagari ya'yanta? Nigeria da yanci muhallin kirki ya gagari ya'yan cikinta? Nigeria da yanci ya'yan cikinta suna farautar yan uwansu? Nigeria da yanci kodayaushe ya'yan cikinta cikin dar-dar suke? A lokacin da girma yake kara kama Nigeria, a lokacin ne take kara komawa baya. Take kara tabarbarewa, Wannan shi Hausawa ke kira da GIRMA BA WAYO! Ba fita murnan cikar shekararta sittin ya kamata mu yi ba. Ba saka rigunan green and white ba, ba zanen green white green a fuska ba, ba raye-raye ba, ba yawaita posting happy independence day ba. Addua ce kadai mafita. Mu tashi mu roka wa kasarmu zaman lafiya da kwanciyar hankali. Mu roki Allah sassaucin wannan tsadar abinci da abun sha. Mu so junanmu. Mu kyautata wa junanmu. Amrah Mashi
  • Hadiza Isyaku KO RUWA NA GAMA BA KI: BABI NA GOMA SHA HUDU Rubutawa: Hadiza Isyaku HAZAKA WRITERS ASSOCIATION ****** "Na amince" Jummai ta faɗa, ba tare da ta yi tunani akan wahalar da ke cikin ciyar da kai ba, ita dai tunda ta samu wurin zama, toh duk abin da kuma zai biyo baya a ganinta ba matsala bane. Ɗakin da tshohuwar ta fito ta nuna mata "Toh ga ɗaki nan ki shigar da kayanki a ciki". Cike da jin daɗi Jummai ta ɗauki jakarta ta nufi ɗakin, kafin ta shiga ɗaya daga cikin matan uku ta miƙe, tare da fara maganar da dole Jummai ta dakata da shiga ɗakin. "Haba Yakumbo! kawai sai ki kama cewa ta shigar da kayanta, ba tare da kin bincika me ke ciki ba, don Allah kada ki zama sanadin shigarmu cikin wani halin, ki barmu mu ji da wanda ya ishe mu". Jummai bata ji haushin maganar matar ba, don ko ita ce sai ta yi fin haka, tunda duniyar a lalace take. Aje jakar kayan ta yi, tare da duƙawa ta zazzage ledar magunguna "Wannan ledar magani ne na ɗana, bai da lafiya", cikin karyayyar murya ta yi maganar bayan ta ɗago. "Toh saura jakar, itama ki buɗe ta a gani", wata kuma a cikin matan ta ce haka. Jiki a mace ta jawo jakar zata buɗe, "Ke rufe jakarki, ki shiga da ita ciki", Yakumbo ta faɗa tana kallon su. Hayayyaƙo ma Yakumbo suka yi ba tare da sun yi la'akari da tsufanta ba, kowa da maganar da take faɗi, sabo da rashin kunyarsu ce ta ce "Ku dai kuka sani, kuma tunda dai ba a kanku zata zauna ba ai shikenan". Duƙawa ta yi ta kwashe ma Jummai maganin, ita kuma ta ɗauki jakar suka shiga ɗakin a tare. Ɗaki ne madaidaici, wanda daga saman rufinsa zaka iya hango sararin samaniya ta wasu ƴan hudoji. Ƙasan simintin kuwa duk ya gurgure. A gefe kuma katifa ce da wasu ƴan ƙullin kaya a kanta, sai kuma tabarma shimfiɗe da kuma randar ruwa. Ajiyar zuciya Jummai ta sauke lokacin da ta gama ƙare ma ɗakin kallo, domin ko da bukkarta take a lalace toh tafi wannan ɗakin daraja. "Lallai da sauran rina a kaba" ta faɗa a ranta. Katse mata tunani Yakumbo ta yi da faɗin "Kin ga ɗakin kamar kango ko?". Murmushi ta ƙaƙaro "A'a" Kai Yakumbon ta ɗan gyaɗa "Toh ga katifa nan ke da yaronki". Jummai ta ce "Toh ku kuma fa", don ta lura katifar ta Yakumbon ce. Yakumbo ta ce "Kada ki ji komai jikata". Godiya Jummai ta yi mata, gefen katifar ta aje kayanta, sannan ta kwanto Ahamad daga goyon, zaunawa ta yi ta fara bashi Mama, ita kuma Yakumbo ta fita wurin sauran matan tana musu nasiha akan ba'a haka, tunda su ma gidannan wani ne ya ji tausayin su ya ce su zauna, bai kamata ba don wani ya zo su riƙa wulaƙanta shi. Cewa suka yi tunda dai ɗakinta ne can ta matse musu. Cikin ɗakin Yakumbo ta dawo, bisa tabarma ta zauna tana fuskantar Jummai da ke ba yaronta Mama. Ɗan shiru ce ta ratsa ɗakin, kowa da abin da yake saƙawa a ransa. Kawar da shirun Yakumbo ta yi, ta hanyar tambayarta sunan ɗanta. "Ahamad" jummai ta ce. "Malam Amadu ne ashe" Yakumbo ta fada tana yar dariya. Ras! Gaban Jummai ya faɗi sakamakon faɗin sunan mahaifinta da Yakumbo ta yi, kai kawai ta iya ɗaga mata, ta cigaba da kukan zuci, addu'ar neman gafarar Allah ta roƙa ma mahaifinta a cikin rai. Fitowar da Yakumbo ta yi daga ɗakin ce taba Jummai damar ɗaga kanta tana kallon rufin ɗakin "Yanzu wannan rufin mai kama da gwagwa idan ruwan sama ya zo ya zamu yi?" tambayar data jefo ma kanta kenan. Kukan da Ahamad ya fara yi ne ya sa ta maido hankalinta gare shi, ɗaga shi ta yi sama tana ƴar dariya "Kukan kuma na miye?" Ƙuri ɗin da ya yi mata ne ya sa ta sumbatar bakinsa sannan ta ce "Sarkin rigima" A cinya ta maida shi tana yi mashi wasa duk don ya yi dariya, sai dai duk yadda ta so ya yi dariyar bai yi ba. Cike da damuwa ta yi magana a ƙasan ranta, "Toh wai ni me ya sa yaron nan bai yi mani dariya, ko dai ya san cewa ta hanyar banza na same shi". Faɗuwa gabanta ya yi, magana ta cigaba da yi da ranta "Toh idan tun yana jariri ya gane kuma yana fushi da ni, toh ina ga kuma idan ya girma" Ido ta lumshe tana jin wani irin ɗaci a ranta, rungume shi ta yi tsam a jikinta ta ce cikin raɗa, "Ka yi haƙuri, ni da Mahaifinka ne muka cutar da kai, ta hanyar samar da kai ba a hanyar da ta dace ba". Wasu ƴan hawaye ne suka gangaro mata a kumatu, ka sa goge su ta yi ta cigaba da kallon Ahamad, ƙasan ranta kuma tana ƙara jin tsanar Habeeb, saboda da bai neme ta ba, da ta hanyar halal zasu haifi ɗansu, tunda har Allah ya hukunta akwai rabo a tsaninsu. Ɗan kukan da ta yi ne ya sa idanunta suka yi nauyi, zamewa ta yi akan katifar tana da ajiyar zuciya, cikin ɗan lokaci kuma bacci ya yi awon gaba da ita. Ta ɗan yi nisa da baccin kenan sai ga yaran gidan sun dawo, wanda hayaniyarsu ce ta falkadda ita, gyara ma Ahamad kwanciyarshi ta yi, sannan ta fito tsakar gidan. Wasu yara ne ta gani waɗanda sadda ta zo gidan babu su, su uku ne, mata biyu sai namiji ɗaya, idan aka haɗa da biyar ɗin ta iske su takwas kenan. Daga cikin Ukun da suka shigo duk hannuwansu ɗauke da roba, biyu da abinci a cikin robarsu, ɗayar kuma babu. Waɗanda suka samo sai murna suke, ɗayar, kuma babbar bata samo ba, fuskarta sai tuƙuburi take kamar zata yi kuka. Tambayarsu aka yi ina suka samo wannan abincin mai ɗan yawa haka. "A wannan gidan ne aka bani" yaron ya ba su amsa yana ta murna, domin wanda ya samo to kasonshi yafi yawa, mafarin wadda bata samo ba take ta fushi. Mamakin yadda yaran suka dabaibaye abincin ne ya kama Jummai, kwata-kwata yaran ma basu lura da ita ba, ta abincin kawai suke. Tambayar kanta ta shiga yi "Me kenan?" Yakumbo ce ta dafa mata kafaɗa, tana son bata amsar tambayar data gani bayyane a fuskarta. A hankali Jummai ta maida idanunta akan Yakumbo da ke faɗin "Toh kin gani, bara ce kaɗai hanyar da muke samun abinci, domin bamu da komai kuma babu wanda yake bamu sai Allah, waɗannan yaran da kika gani rabon su da abinci tun safe, shima sai dalilin wani Alhaji da ke sadakar Fanke da ƙosai suka samu kalacin, ƙila da har yanzu basu ci komai ba". Ƙuri Jummai ta yi ma yaran, ƙasan ranta tana jin wata masifar tausayinsu, musamman da taga yadda suke tsakurar abincin suna ci duk don kada ya ƙare. Ido ta lumshe tare da matse hawayen da suka cika mata ido lokacin da ta ga wani yaro ya tsince shinkarshi biyu da ta faɗi ƙasa ya maida a cikin roba. Tabbas ta yi rayuwar yunwa, kuma da alamun zata koma a cikinta, to amma a wannan karon ba kanta take tausayi ba, ƙananun yaran da basu san babu ba su take tausaya mawa. Cigaba da magana Yakumbo ta yi "Ina tausayinki a kan wannan rayuwar, don haka a ganina ki ɗauki kayanki ki nemi gidan da yafi namu". Kai jummai ta girgiza tare da fashewa da kuka "Ba inda zan je domin nima irin rayuwarku nake, banbancin shine ni azabtar da ni aka yi yunwa, ku kuma Allah ne ya jarabce ku da ita, ina tare da ku har zuwa lokacin da Allah zai kawo mana mafita". Gaba ɗaya matan gidan da yaran kallonta suka riƙa yi, ruƙo ta Yakumbo ta yi "Toh Allah ya kawo mana mafitar". Wasu daga cikin yaran suka ce "Amiin". Abincin da aka ɗan zubo musu a marfi ita da Yakumbo ne aka miƙo musu, wanda dukan shi bai wuce loma ɗaya ba. Godiya Yakumbo ta yi bayan ta karɓa, miƙa ma Jummai ta yi "Karɓi ki ci" kai kawai Jummai ta girgiza don ba zata iya magana ba. Matsa mata Yakumbo ta yi akan ta karɓa, amma ta ƙiya, duk da kuwa yunwar da ke cikinta. Jin motsin Ahamad ne ya sa ta komawa cikin ɗakin, goya shi ta yi sakamakon magarib da ta ƙarato. Fitowa ta yi da nufin yin arwalla, sai dai gidan ba ruwa ko kaɗan. Tambayar ruwa ta yi, Yakumbo ta ce "Bamu da ruwa, amma bari in ɗebo maki a wurin famfo". Tare da Yakumbon suka tafi ɗebo ruwan, a hanyarsu ta dawowa ce suka ga wata Mai Awara. Kada fa ku ce na cika faɗin Awara, Amanar dake tsakanina da ita ce ta sa nake ta haɗa Jummai da ita. Sallah suka dawo suka yi, sannan ta ɗauki Ɗari biyar a cikin ragowar kuɗinta ta siyo musu Awara ta duka. Tasu ita da Yakumbo ta ɗiba, sauran kuma ta miƙa ma matan gidan da yaransu, sai gashi sai washe baki suke suna mata godiya, wanda da farko ba haka ba. Bayan ta dawo ɗaki Yakumbo ta ce mata "Kin ga ki lallaɓa kuɗinki, kowa tashi ce ke fisshe shi a gidan nan". Murmushi kawai Jummai ta yi, don muddin tana da abin badawa, toh ba zata hana yaran can ba. Hira suka shiga yi bayan sun gama cin Awarar, aikuwa Yakumbo ta bata labarin irin ɓarnar da kidnappers suka yi musu a gari. Ta ce "Sun kashe maza, sannan suka kwashi dukiya da mata, yanzu haka a Ƙauyenmu da ƙauyukan da ke kusa da mu duk sun tarwatse, kowa ya kama gabanshi, wasu sun tafi gidajen danginsu, irin mu kuma da bamu da kowa a birni muka yi ta gararanba, har Allah ya sa wani bawan Allah ya ji tausayin mu ya bamu wannan gidan mu zauna". Sosai Jummai ta tausaya musu akan halinda suka samu kansu a ciki, tambayar Yakumbo ta yi alaƙarta da waɗancan matan, Yakumbon ta ce "Gari ɗaya kaɗai ya haɗamu, su iyalan mutum biyu ne, an kashe ɗaya, ɗayan kuma ba'a san inda yake ba". "Ni kuma bani da kowa sai Jikana Namiji, shi kuma Yana Lagos neman kuɗi, bai kuma san inda nake ba, yanzu tunda ba waya". Cike da tausayawa Jummai ta ce "Lallai kuna cikin damuwa, Allah ya kawo muku ɗauki" Yakumbo ta ce "Amiin" "Toh ke kuma matsalar miye ce a garinku?" Yakumbo ta tambayi Jummai. "Mu kuma boko haram ne" Jummai ta faɗa, da yake ta yi musu ƙaryar Maiduguri take. "SubhanaLlahi" Yakumbo ta ce, don tana jin labarin boko haram, wanda ɓarnarsu ma ta fi ta kidnappers Tamboyoyi ta shiga yi mata ina mahaifanta, da mijinta suke. Tunani Jummai ta shiga yi akan ƙaryar da zata yi ma Yakumbo wadda ta yi daidai da damuwarta. Mahaifina ya rasu, mijina kuma ban san inda yake ba, mahaifiyata kuma.." sai ta yi shiru "Me ya samu Mahaifiyar taki", cikin muryar tausayi Yakumbo ta tambaye ta. Kasa bata amsa ta yi, sai ma kuka da ta cigaba da yi, don ba zata yi ƙarya a kan mahaifiyarta ba, sannan ba zata iya faɗin asalin inda take ba. Tausayin ta ne ya kama Yakumbo "Ba zan matsa maki akan sai na ji labarin mahaifiyarki ba, amma ki yi haƙuri, Allah ya jiƙan mahaifinki, mijinki kuma Allah ya bayyanar maki da shi". "Ba Amiin ba" Jummai ta ce a ranta, akan Allah ya bayyana mijinta da Yakumbo ta ce, domin ba ta da buƙatar shi a yanzu. Shirin bacci suka yi, Yakumbo ta kwanta a kan tabarma, Jummai kuma ta kwanta ita da ɗanta a kan katifa. Kasa bacci Jummai ta yi, saboda tunanin mahaifiyarta da kuma ƙannenta, ko wane hali suke ciki yanzu, tunawa da Mahaifyarta ba son ta take ba ya kawar mata da tunanin su. Kukan Yunwa da yaran gidan ke yi ne ya falkar da Jummai, tana buɗe ido ta ga har gari ya fara haske, a gaggauce ta fito da nufin yin alwalla. Sai dai kuma gidan ba ruwa ko kaɗan. Bokiti ta ɗauka ta nufi inda suka ɗebo ruwa a jiya. Abin kallo ta zama a wurin. Bokitinta ta sanya a layi, sannan ta koma gefe ta tsaya. Murya ƙasa-ƙasa ta ji wata budurwa na magana da ta kusa da ita "Ke ƴan gudun hijirar can fa cewa aka yi mayu ne, ɗan gidan Malam Idi da ya rasu tsohuwar gidan ake zargi da lashe shi". Ras! Gaban Jummai ya faɗi, "Yanzu da mayu nake zaune ban sani ba", gazgata maganarsu ta yi ta hanyar tuna yadda Yakumbo ke ta nan-nan da ita, ashe don ta lashe su take yi. "Wallahi ba zan iya rayuwa da mayu ba". Gabanta na wata irin faɗuwa ta ɗauki ruwan ta tafi, a hanya zuciya ta yi ta saƙa mata Yakumbo na can ta lashe Ahamad. Tun a bakin zaure ta aje bokitin tare da nufa ɗakin da sauri. "Kada ki taɓa mani ɗa" ta faɗa a cikin ƙaraji, lokacin da ta ga Yakumbo zata ɗauki Ahamad da ke kuka. Fasa ɗaukar shi Yakumbo ta yi, saboda ta gane abin da take nufi, da sauri Jummai ta ɗauke shi tana dudduba shi. Murmushi Yakumbo ta yi ta ce "Jikata kenan, kema kin gamsu da maganar ƴan waje cewar mu mayu ne ko?". Shiru Jummai ta yi tana ta huci, ganin bata yi magana ba ya sa Yakumbo cigaba da faɗin "Tunda aka fara jifarmu da wannan ƙazafin bamu taɓa kare kanmu ba, don mun san ba kowa ne zai yadda ba, amma kuma mu da mayun ne da talauci bai kama mu ba wallahi". Nazari Jummai ta shiga yi, sai ta gane rashin kyautawarta, kuma ko da Mayun ne ai ba haka ya kamata ta yi mata ba. "Ni fa ba haka nake nufi ba Yakumbo" Jummai ta faɗa idanunta a ƙasa. Kai kawai Yakumbo ta gyaɗa don abin na matuƙar damun ta, "Haba Jikata, ni fa ba yarinya ba ce". Haƙuri Jummai ta yi ta bata, don ta fahimci ƙazafin mutane ne kawai, da yake tana da sauƙin kai ta ce "Shikenan, amma ki riƙa nazari kafin ki yanke hukunci". Labari ta bata akan yadda abin ya samo asali, satinsu uku da zuwa wasu yara suka rasu, sai aka ce sune suka kama su, tun daga nan ƴan unguwar suka fara tsangwamar su, ɗan daka da wankin da suke kawo musu, suka dena kawowa. Yakumbo ta ce "Ƴar nan in yi maita in samu me, wallahi ko yunwa zata kashe ni ba zan iya maita ba, amma kin ji cewa ake ni ce shugabansu", kamar Yakumbo zata yi kuka ta ƙarashe maganar. Magana mai daɗi Jummai ta cigaba da faɗa mata, ƙarshe ta tabbatar mata da sai ta ƙwato mata haƙƙinta, tunda ta riƙe fuskar yarinyar da ta yi maganar. Asabe kuwa na can ta koma kamar zautacciya, duk wanda ya zo yi mata jaje sai ta riƙa faɗa mashi cewar "Wallahi ni ce silar tafiyar ƴata, nina juya mata baya a lokacin da take buƙata ta". Da Alhaji Mainasara ya zo tana faɗin haka ya ce "Ai ba Jummai ce kaɗai kike da silar tafiyarta ba, hatta mijinki Malam Amadu ke kika kashe shi ba kowa ba". Faɗa sosai ya riƙa yi mata duk da ƙanwarta yake aure, amma shekarun da yake dasu suka sa shi rufe ido ya yi ta mata faɗa. ya ce "Ke da Mairo baku da hali ko kaɗan, ku baku san rangwame ba a rayuwarku, duk wanda ya yi ba daidai ba sai kun taka shi iya son ranku, kuma ba'a haka, domin ba wanda baya kuskure a rayuwa". Kuka Sosai ta cigaba da yi, Kabiru dake gefen Alhaji Mainasara ya ce "Ai baki ma fara kuka ba", don yanzu babu mai tausayinta saboda azabtarwar da ta yi ma Jummai, wadda da bakinta ta riƙa faɗi. Haƙuri Alhaji Mainasara ya bata, sannan ya tabbatar mata da zai sa a bincika a garuruwa. Haka aka yi kuwa, kusan duk jihohin Nigeria sai da aka bada cigiyar Jummai, amma ko mai kama da ita ba'a gani ba. Ƙin faɗa ma Asabe aka yi ba'a ganta ba, sai dai aka ce ana ta cigiyar, duk yadda ta kasance za'a faɗa mata. Ƙawar Hajiya Mairo kuwa, tunda ta ƙyalla ido ta ga Habeeb ta shiga kimtsa yadda za'a haɗa shi da ɗiyarta. Da yamma su duka suna zaune a falo hada Hajiya Mairo suna hirar Habeeb. Bayan hirar ta ɗan nisa ta dubi Hajiya Mairo a tsanake "Kin san da gaske nake fa na ba Habeeb Salma". "Ke Hajiya Sa'a" Hajiya Mairo ta faɗa tana dariyar yaƙe, don idan ba ƙaddara ba bata fatan haɗa ɗanta aure da Salma, don a kan idonta motoci ke ɗaukarta suna tafiya. Hajiya Sa'a ta ce "Allah kuwa, in dai Habeeb ɗin ya amince, kin san an dena yi ma yara dole a kan aure". "Hakane abin da ke Alkhairi Allah ya tabbatar da shi" Hajiya Mairo ta faɗa. Hira suka cigaba da yi, a mafarkin ƙaryar Hajiya Sa'a ta ce "Kin ga kuwa idan Allah ya haɗa, sai a ɗaura auren a tura mashi ita can, kin ga karatu ga matarshi". Dariya kawai Hajiya Mairo ta yi, don kallon mahaukaciya take mata, a yadda Habeeb yake cikakken Namiji, ba zata yadda ya aure kwashe-kwashen mata ba. Da daddare bayan Hajiya Mairo ta shige ɗakinta ta kulle, Whatsapp ta shiga suka fara vedio call da Habeeb, don tafi son ta ganshi Live, hankalinta yafi kwanciya. Ganin yadda yake ta ramewa ta ce "Wai lafiyanka kuwa Habeeb, kullum sai ƙara ramewa kake, ko baka da lafiya?" Ido ya lumshe tare da girgiza kai "Lafiya ta Umma, karatu ne kawai", duk da ƙarya yake, ko kusa bai da lafiyar zuciya, saboda kullum cikin kewar Jummai da ɗanshi yake. "Hmm" kawai ta ce don ta san ƙarya yake, "Ka dai je likita ya duba ka, don wannan ramar ba ta lafiya ba ce. "Toh Umma zan je Insha Allah". Hira suka cigaba da yi cikin raha, har take bashi labarin Hajiya Sa'a fa da gaske ta bashi Salma. "Allah ya sauƙe mun in auri wannan yarinyar" ya faɗa ranshi a ɓace. Cikin zaulaya ta ce "Kai kuwa Habeeb, Salma ai bata da matsala". "Haba Umma, ai ba Salma ba, ni yanzu babu wata yarinya da zan iya ɓata lokacina a kanta, bare kuma har in aure ta" "Kenan ba zaka yi aure ba" ta sake tambayar shi. Kai tsaye ya ce "Zan yi mana Umma, aure na da Jummai zan maida" Take kuwa ta haɗe rai "Wace Jummai, bayan wadda ta koma yawon karuwancin ta". "Kamarya ta koma karuwanci, Umma ita fa ba yadda kike zato bace", cikin jin haushin wannan maganar ya yi maganar. Tabbatar mashi ta yi da Jummai ta gudu, don tuni ƴan gulma sun bata labari, kuma har a Tv taga cigiyar ta. Wata irin kiɗima Habeeb ya yi, bai san sadda ya tsinke kiran ba, tare da dafe kai ya shiga salallami, "Me ya sa Fateema zata yi haka, ina ta tafi, kuma wane yanayi ta samu kanta a ciki?" Tambayar da ya yi ta jefo ma kansa, wanda Jumman ce kaɗai zata iya bashi wannan amsa. Ita kuma tana can wurin neman abin da zasu ci ta samu wanke-wanke a wani gidan abinci, ba don ranta yaso ba take aiki a wurin, sai don ta rasa yadda zata yi. Wani mutumi ne ya sa baki aka ɗauke ta aikin, don da farko matar da ke da gidan abincin ƙin ɗaukarta ta yi. Da wannan aikin ne take ciyar da kanta, har ma ta taimaka ma su Yakumbo. Hakan ya sa shaƙuwa mai ƙarfi ta shiga tsakaninta da sauran matan gidan, har ma yaransu, tunda duk wani sauran abinci da aka yi a can su take kawo mawa. Wannan mutumi kuwa kullum cikin kyautata mata yake, duk sadda ya zo siyen abinci sai ya ce ita zata kawo mashi. Ta ce "Ai ni aikina wanke-wanke kaɗai", kafe ta ya yi da idanu, daga bisani ya ce "Wannan jikin naki mai kyau ya fi ƙarfin wanke-wanke". Murmushi kawai ta ta yi, ya ce "Je ki ce ma Hajiya na ce ta baki abinci ki kawo mani". "Toh" ta ce tare da juyawa ta tafi, ji ta yi a jikinta kallonta take, waigowa ta yi don tabbatar wa, aikuwa suka haɗa ido, girar da ya ɗaga mata ce tasa ta saurin juyawa. "Wancan mutumin anya ba ɗan iska bane", ta faɗa a ranta lokacin da ta isa wurin Hajiya. Karɓo abincin ta yi ta kawo mashi, idanunsa cikin nata ya ce "Toh zauna mu ci". Da dariya ya ƙarasa maganar. Ido ta ɗan zaro tare da girgiza kai tana dariya. Ɗan shagwaɓewa ya yi tare da faɗin "Toh ki zauna, ina kallon ki ina cin abincin, idan ba hakaba ki ɗauke abincin". Ƙin zama ta yi ta juya tana dariya, dariyar shima yayi, ya bi ta da idanu. shirin komawa gida Jummai ta yi, don ta baro Ahamad wurin Yakumbo, kuma ta san zai buƙaci mama a yanzu. Zagayawa ta yi don bata son mutumin ya ganta, ashe ya ganta har ya bi bayanta ma ya ga gidansu. Da yamma liƙis suna cikin Hira ita da matan gidansu aka aiko yaro da ana kiran Jummai. Tsokanarta matan gidansu suka shiga yi, wai daga fara zuwa aiki har ta yi kasuwa. Dariya tayi, sannan ta fita, ganin wannan mutumi ya sa ta tokarewa a bakin ƙofa. "Kin yi mamaki ko?”, ya faɗa yana dariya. Ƴar dariya ta yi, cikin ranta kuma ta ce "Ko maye ne kai, dole ka shafa ma kurwata lafiya". Gani ta yi ya ƙaraso inda take ya tsaya, cike da kunya ta gaishe. Amsawa ya yi, sannan ya fara janta da hira ta hanyar tsokana, ita dai ba abin da take sai dariya. Ganin ta saki jiki dashi, sai ya bijiro mata da abin da ya kawo shi, cewar yana sonta. Haƙuri ta bashi, tare da tabbatar mashi da tana da aure, don ita bata san da wani sakinta da Habeeb yayi ba, kuma duk shakiyancinta ba zata yi soyayya alhalin da igiyar aure a kanta ba, duk da irin ƙin da take yi ma auren. Bai ji daɗi ba, amma sai ya cije ya ce "Ba komai, ai za'a dai riƙa gaisawa ko". Ta ce "Insha Allah", bankwana suka yi, ya tafi. Cikin gidanta koma tare da ba ƴan gidansu labarin yadda suka yi da mutumin, su sai a ranar suka san tana da aure. Shi kuwa duk da Jummai ta faɗa mashi tana da aure bai dena kyautata mata ba, duk lokacin da ya je gidan abinci ita yake fara nema su gaisa, kuma kusan kullum sai ya yi mata Alkhairi na kuɗi ko wani abu. Da ta nuna ya dena yi mata kyauta hakanan sai ya ce "Ai ba don ina son ki nake miki kyauta ba". "Sai don me?" ta tambaye shi. Amsa ya bata da "Sai don ina tausayinku ke da mutanen gidanku, kuma Alherin da nake maki a zahiri ke kaɗai nake ba, amma a baɗini hada ƴan gidanku, domin ina da yaƙinin kina taimaka musu" Murmushi ta yi tare da gode mashi, domin yana matuƙar taimaka musu, domin rabon da su kwana da yunwa har sun mance, kullum fatan Alkhairi suke yi mashi, domin ya zama ma kamar ɗan gida, lokaci bayan lokaci yana kawo musu ziyara har gida, kuma a zahiri kamar ya aje batun soyayyar da yake ma Jummai a gefe. Ita kuwa Jummai duk yadda kake zaton hankalinta a kwance yake, domin daidai gwargwado ita da ɗanta sun murje sun yi kyau, toh ba haka bane, domin kullum da tunanin gidansu take kwana, tambayar ta kullum take ma kanta "Wane hali ahalina suke ciki?". Wannan damuwa bata ƙaru ba sai ranar da wannan mutumi ya same ta har gidan abinci, tare da bijoro mata da muguwar buƙatarshi a kanta. Bayan sun gaisa kamar yadda suka saba ya ce "Wata magana nake son muyi, fatan zaki bani dama". Ba tare da tunanin komai ba ta ce "Na baka dama". "So nake mu ƙulla alaƙa mai ƙarfi da ke, wadda zaki ƙara samun mafita a cikin rayuwarki". Cikin rashin fahimta ta ce "Alaƙa kuma, wace iri? " "So nake ki bani kanki" Wata irin faɗuwa gaban Jummai ya yi, "Me ka ce" don bata son yanke mashi hukunci sai ta sake ji daga bakinshi. "Cewa na yi Ki bani kanki…." Ku biyo ni a ci gaban labarin in Allah Ya yarda. MAMAN MU'AZZAM
  • Hassana Zakariyya MAIDARU Duk wacce take buqatar maganin infection ga feminine wash Idn maganin mata kike buqata sadidan idn Kika samu feminine wash kinwuce wajen, saidai kawai kinemi kayan marmari kifara Sha. Tabbas duk mace da Bata amfani da feminine wash anbarta abaya domin yahada duk wani abu dakike buqata domin tsabtace gabanki da kuma samarwa kanki lafiya da kariya. Ynx hr likitoci suna rubutawa patient masu fama da matsalar qaiqayin gaba ko discharge,Yana taimakawa sosai lokacin period domin dauke qarnin jini to aikinshi ba nan kadai yatsaya ba hr da Samar Miki da niima abundai sai wadda tayi amfani dashi duk wacce ta gwada a group din nn nasan zata bada labarinshi. Budurwa Matar aure Bazawara Hr maxa masu fama da basir Gynecologically tested and approved Duk wacce take buqatar Kuma tana ga WhatsApp number ta 09039063492 akwai audio na testimony dayawa idn bakya WhatsApp Kuma kinaso kiyi cmmnt da location dinki
  • Suwaiba Moh'd (Mrs yarima) KISHIYAR BALBALINA Page 1 to 5 NA SUWAIBA MOH'D GOMBE (Mrs Yarima) Real Mrs Yarima WhatsApp 08178287947 GODIYA: Godiya ta tabbata ga Allah subhanahu wata'ala, tsira da amincin Allah sutabbata ga fiyeyyen halittu annabi MOHAMMAD S.A.W da sahabbanshi da 'iyalenshi. GARGADI: Ba'ayarda wani ko wata yacanja wani 'abu daga cikin wannan littafin ba, akiyaye. GAISUWA: Gaisuwa ga dukkannin daukacin members na MRS YARIMA HAUSA NOVELS, Happy New Year 2018. MASOYANA: Masoyana 'ina 'alfahari da ku, nagode sosai, naga sakonninku sun 'iso, nayi farinciki sosai da nuna kaunarku gareni, ina muku fatan 'alkhairy 'aduk 'inda kuke, Subee Mrs yarima ce. DA SUNAN ALLAH ME RAHMA ME JINKAI! Sauri takeyi domin taga ta kammala girkin da tadora, ganin har 'anfara kiraye-kirayen sallar magriba 'awasu masallatan, wanda kuma hakan yakara tayar mata da hankali matuka. Tasan yaude kam zatasha fada sosai 'awajen sirikar tasu, duk da cewar tasaba da hakan, domin 'inda sabo yazame mata jiki. Kular da tafi kyau 'acikin kulolin nata tazabo domin zuba mata 'abin da ta girka. Dankalin hausa ne ta soya, kasancewar yau ranar litinin, domin tana 'azumtar wa'yan nan ranaku, se kuma farar shinkafa da tadafa tayi mata miyar stew da dan'yen kifi shima tazuba. Ahanzarce takwashe kulolin tanufi han'yar fita, domin kaiwa sirikar tasu. Zaliha ce tsaye 'abakin kofar, tana ganinta tawashe baki! Sannan tace bade har kin kammala ba? Ay nagama kuwa tace tana mamakin hali 'irin na Zaliha, dazufa tagama gayamin bakaken maganganu kuma har take 'ikirarin cewa 'idan nasakeyi mata magana se naga mugun sakamako, baki ta tabe tare da sake rayawa 'acikin ranta to 'ai 'ita tayimin magana. Miko hannun da tayine tana fadin kawo natemaka miki tunda gidan zanshiga yakatsewa Haleematu tunanin da takeyi. Aah, kibarshi kawai Maman Saif tace, yanzu zan mika mata nashigo. Aah 'ay baza'ayi haka ba Zaliha tasake cewa 'ayayin da takarasa karban kulolin dake hannun Haleematu tafice. Ido kawai tabita dashi har tafice daga zauren gidan nasu, cike da takaicin hali 'irin na matar wan mijin nata takomo cikin gidan. Agurguje tadora wani 'abincin domin tarban mijin nata, don tasan 'abin da ta girka wa mahaifiyar tashi ba 'irin 'abincin da yakeso ba ne 'awannan lokaci. Saboda hakane tafara hanzartawa don ganin takammala kafin yashigo gidan, sannan tadauro 'alwala domin gabatar da sallar magriba. ************Mrs yarima ce ACAN GIDAN SIRAKANAN NASU KUWA: Zaliha tana dire kulolin 'abincin da Haleematu ta girka 'agaban sirikar tasu tawuce kitchen tadauko filet. Tana dan murmushi 'irin kuma na nuna 'alamun jin nauyi da kunya tace Inna don Allah adan sammin 'abincin, wallahi tun da Haleematu tafara girkin nan raina yabiya. Kular Inna taturo mata, sannan tace kidibi wanda ze'isheki kici 'anan base kinshiga gidan naku dashi ba. Cike da tsanar Haleematu 'afuskar Inna tacigaba da cewa nide banga miye 'atattare da yarin'yar nan ba da har Idrisa zedinga kin duk' wani 'abin da yan'uwanshi suka gani suka gayamishi ba!!! Yarin'ya ga dan banzan rowa da bakin hali, yanzu ko don cikin dake jikinki 'ay zataji tausayin ki. Hmmm! Inna kenan Zaliha tace 'ayayin datakai loman 'abincin bakinta tacigaba da cewa, ay duk' abinda za'afada babu me yarda se ni da nake zaune da 'ita gida daya. Ni bansan menayiwa Haleematu ba Inna, wallahi bata sona kwata-kwata, amma 'abin da yake bani mamaki shine 'agabanku se tadinga nunawa yaron nan Saif kamar gaske, kinga kuwa 'in muna gida ko kallonmufa batayi Inna. Inna ce takatseta da cewa 'ay munafurcin kenan, kede kibar mutum me shuru-shuru, domin be 'iya mugunta ba. In banda mugunta 'irin na Haleematu 'aiko domin cikin da ke jikinki zata dinga sammiki 'abin da ta girka, ko da yake 'ay ba'kin ciki baze barta ba Inna tasake cewa. Hirarsu sukacigaba dayi har suka kammala cin abincin, sannan Zaliha tamike tanufo cikin gidan nasu. ************Mrs yerima ce
  • Rabee'atou A Oumar (Pinky) 🌖 *BAMBANCIN HALITTA* 🌖 ©️℘ıŋƙყ wattpad😛inkylady222 Email😲umarrabiatu@gmail.com 02 *Kyanko* *2001* ƙaton fili ne da ya ke cike maƙil da jama'a, a na ta hayaniya a na maida yadda akai. tsawon lokaci kafin wasu murguza murguzan mutane da babu komai a jikinsu sai 'dan fantare da su ke a k'ugunsu, su ka buɗe ƙatuwar muryar da Allah yai masu su ka fara kwarara ihu da ke shaidawa jama'ar wurin Ambarama ta iso. A take kowanne yaja bakinshi ya rufe suka sunkuya cike da girmamawa har ta ƙaraso ta zauna a kujerar da ta ke ta ƙaton dutse ce aka lanƙwasa sannan akai mata ado. Wurin ya ɗau wani kalar shirun da ko allurar ka ta faɗi zaka iya jin sautin faɗuwarta. Bayan yan daƙiƙu da zaman ta waɗannan margaza-margazan mutanen su ka iso filin jaye da wani tsoho da ke ɗaure da kaca ya na tafiya daƙyar jikin shi duk ya farfashe. A ka Duƙar dashi gaban Ambarama ya sadda kanshi ƙasa Ɗaya da ga cikin mutanen Ambarama ya fara jawabi. "Kamar yadda kuwa ya sani game da zunibin da Ayuroro ya aikata a nahiyar nan da sauran nahiyoyi maƙwabtanmu, wanda sanadiyyar hakan ta jawo ɓarna da sanadiyyar rayuka aruaru ta kuma jaza tarzomar da ba a daɗe da kwantar da ita ba." "..a yanzu bayan shekaru ukku kamar yadda shari'a da doka ta tsara tare kuma da taimakon sarauniya mai girma Abin kwatance Ambarama ta tanada, hukun cin Ayuroro na farko zai hau kan shi." "Lafiya, tsayon rai Ambarw" "lafiya mai girma Ambara" jama'ar wurin ke faɗi cikin amanna da duk wani hukuncin ta. Mutanen ta suka ɗaga hannu akai shiru. Ɗaya da ga jikin su ya taho da wani ƙoƙo ya aje gaban ayuroro. "Dakata!" Ambarama ta faɗi akaron farko ta na kallon Ayuroro da ke niyyar ɗaukar ƙoƙon. Ya tsaya jikin shi na ɓari hawayen shi duk sun bushe. A yanzu bai da sauran hawayen da zasu kuma zubowa kuma, ya riga da yasan abin da zai faru a ƙarshe kenan. Ahalin shi sun zama cutuwa a gareshi, sun jefashi cikin bala'en da bai isa ya fidda kan shi ba. "Ka koma a salin halittarta kafin ɗaukar hukunci." Maganar ta ta katse tunanin shi. Ta na rufe baki ya haɗe hannuwanshi wuri ɗaya tare da girgiza sai ga ƙaton maciji sharɓeɓe ya bayyana. An riga an gama duk wani bayanin da za ai, kowa yasan hukuncin abin da ya aikata. Ya sulala ya kafa kanshi a ƙoƙon ya ruza halshenshi ya surɓe abin da ke ciki. Dandanan ya fara yamutsewa ya na komawa ɗan ƙarami kamar sabon macijin da aka haifa. A cikin jinga jingan nan wasu suka taho da wani abu mai saƙa-saƙa mai shara-sharar da ana hangen abin da ke ciki tamkar gilas, suka aje gaban macijin sannan suka ɗauke shi su ka saka a ciki suka maida marfin suka rufe. Ambarama ta kalli abun wani abu kamar walƙiya ya fito da ga bakin ta ya bugi abun ƙara ta karaɗe wurin har ana toshe kunnuwa. Daga nan sai ta bada umar nin a ɗauke abun ta tashi. Kowa ya watse, wasu fuskarsu da alhini. ***** ****** ***** Ambara na komawa gida ta shige ɗakin ta tare da sallamar masu hidimta mata ta buga ƙara, ihu da kukan baƙin ciki. Ta saka ranta da bayyanar duk gaskiyar da ta ke son sani ga lamarin nan ko dan ta san yadda zata bullowa lamarin ta haɗa iyalanta. A matsayinta na shugaba a yanzu amma ace ba ta da kowa nata bata da jinin da zata kalla ta ji daɗi. Kuka ta ke mai cin rai, kukan kaɗaici. Ta ɗauki lokaci mai tsawo ta na wannan kukan kafin ta gaji ta bari sannan ta bada dokar ba zata ga kowa ba har tsawon kwana bakwai. *Mafarin komai* *1999* Zaune ta ke bisa ƙaton dutse ta zura ƙafafuwanta cikin makeken ruwan da ke wucewa, ta kuma zuba mashi idanuwa a zahiri. A kai-akai ta ke jefa ƙananun duwatsun da ke dumtse a hannunta cikin ruwan. Kusan Sati biyu kenan amma ta kasa mantawa da maganar mahaifiyarta 'maima' _idon ki ya rufe da ganin gaskiyar kalamaina 'Farfar', kin makance da soyayyar da ba zata amfane ki ba._ _ya zama dole kuma ki goyi bayana na mulki *kyanko!*_ ta saka hannu ta gyara gashin kanta da iska ke kaɗowa a fuskarta. Ta sunkuya ta sake dumtso duwatsun saboda ƙarewar da na hannunta sukai. Tunani ta ke son yi, mafita ta ke so. Amma ta yaya? wanda ya ke bata dukkan mafita a yawan lokutta,yanzu matsalar da ga nan ta fito. Jikinta ya bata kallonta ake, dutsen da ta ware za ta jefa ta fasa. "Idan ka ci gaba da tsayuwa a nan, kwarjininka zai iya saka tunani na gushewa" ya tako a hankali cikin tafiyarshi ta cikakkun maza masu jini a jika. Ya saka hannunshi ya tattare gashinta ya maida shi gefen wuyanta. Sannan ya leƙo da kan shi ta ɗayan ɓarin har ta na shakar numfashin shi ya ce "A mabiya kyanko ne kawai challa ke da kwarjini. A wurin ki kuma tamkar jaririn da ki ka haifa ne" ta lumshe idanuwanta ta buɗesu a hankali. Sannan ta kamo hannunshi ya zagayo ya zauna gefen ta. "Sai ki ka zo ke ɗaya, ki ka baro ni ko. mai ya sa?" Ya faɗi sa'ilin da ya sauke jikkar da ke rataye a wuyanshi. "Ha ka kawai yau na riga ka zuwa kafin cikar lokaci" "To shikenan in dai ba laifi na yi ba da sauƙi" ya ɗebo duwatsun ya fara jefawa. Ta kalli yawan ruwan yadda suke tafiya har ba a iya ganin ƙarshe su. Ta ce "Challa" "uhm?" ya amsa ya na kallonta. "Ni ina son na tsallake ruwan nan ina son shiga.." Sai ta ɗan yi shiru ta na tunani "Ya sunan nahiyar?" "Mwagbo" ya bata amsa ya na murmushi. "Yauwa mwagbo.. ina son ganin yadda su ke rayuwarsu. Wai ba irin ta mu ba? addininsu daban?" ya gyaɗa mata kai. "ina son shiga" "kar ki damu babu in da ba zaki zagaya ba ma idan lokaci ya yi _Boidi_ (princess)" Sai ta yi murmushi ta ce "wa ne kalar addini suke?" "kayya dai! Ba ni da ikon gaya maki akan hakan Boidi a yanzu" Ta tsuke fuskarta ta mik'e ta na had'e rai, maganar maima na dawo mata. ' _ke fa ba za ki ta b'a samun cikakken 'yancin da za ki ziyarci dukkan inda kike so ba Matuk'ar mulkin kyanko ba naki ba ne_ ' Ta cije leb'en ta na k'asa ta na jin haushin challa, mo ba komai ai an riga an masu baiko, zuwa yanzu ya ka mata ace tasan duk wani abu da ta ke son sani gane da ko wace nahiya. Ya ruk'o hannunta. Ta juya mashi ba ya ta na k'in kallin shi. "haba Boidin challa, bai kyautu mu samu sab'ani a kan abin da kin riga kin sani ba. Babu wanda ya ke da damar tsallake nahiyarmu ko jin halin da wata nahiya ta ke ciki nusamman mwagbo, sai jinin mulkin kyanko. Ke kuma duka mai ya rage? Da ga munyi aurenmu kin haihu shikenan fa zaki san koma miye. Ki bar damuwar nan kin ji?" Ta gyad'a kai. "yauwa yimun murmushin nan in gani" Ta murmusa ba dan ta so ba. Ta na son challa sosai a gefe d'aya kuma ta fara kwad'ayin abin da mahaifiyarta ke kwad'aita mata gaje kyanko gaba d'aya. Ya jawo jikkar da ya zo da ita ya d'akko k'aton ganyen da ya nad'o gasasshen nama a ciki. K'amshin naman ya bugi hancinta, yawunta ya tsinke ya zarce mak'ogoron ta. Idan akwai abin da ta fi so gasasshen nama ne. Kasancewar a gaba d'aya nayihar babu mai ikon cin naman da aka dafa sai masu mulkin nahiyar, duk kuwa da naman shine abincin su kawai a ko yaushe, hakan kuma bai dame su ba tun da haka tsarin yake haka kowa ya tashi ya ga a nayi. Idan kana da wani had'i da su ko wani a ciki ya baka za ka iya ci amman kai ba ka da damar gasa nama. "mu ci abincin nan kar yai sanyi" Ta matsa kusa da shi ta zauna su ka fara Cin abincin, su na yi yana mata fira har suka gama. Sai da duhu ya fara sannan su ka bar wurin har gida ya raka ta inda ko ina zagaye ya ke da duwatse da su ake zagaye ko ina afidda gida je a cijin gidan ma dasu ake fidda d'akuna. A gaba gudansu sun dad'e suna fira kafin yai nata sallama ya tafi. "ni dai ban ga amfanin soyayyar nan ba farfar" Tai dariya ta zauna kusa da ita. "mama kenan, kin san challa ya na so na sosai Ni ma kuma ina son shi. Bayan nan ana darajamu da girmama mu mama gashi zan shiga gidan shugaba amatsayin suruka, challa zai zama shugaba.." "ke ni rufe mani baki" Ta katse ta. "kibar ganin kamar zaki samu duk ikon da kike tunani. Eh zaki samu sosai amma ba komai ba, idan ki na ganin abin da na ke gaya maki k'arya ne ki jira ki auri challan. Ina nai rantse maki da mahaifinki sai kin yi nadamar k'in bani had'in kai da ki kai" Farfar tai shiru ta na juya maganar mahaifiyarta a ranta. Ita ma maima ba ta ce mata komai ba ta barta tai tunanin da zai fisshesu su duka. Tunanin yai mata yawa ta kasa karkata ga b'angare d'aya sai kawai ta tashi ta shige d'akin da babanta ke had'a magungunan shi. Ya na zaune ya juya baya ya na duba wasu shafukan takardu rubutun ciki mai haske. Ya na dubawa ya na had'a magungunan shi. Tsaye ta yi har ya gama ya rufe maganin acikin k'atuwar kwalba sannan ya juyo ya fuskance ta. "a rayuwa ba komai kake so kake samu ba duk kuwa ga yadda ka so abunnan. Hakuri da yadda tsarin rayuwa ya zo maka shi zai sa ka tayu cikin farinciki da kwanciyar hankali" Ta sadda kanta k'asa ta na murmushi Ta ce "to baba, nagode k'warai" Ya jinjina kai, sanna ya ciga ba da yi mata nasiha mai hannun ka mai sanda ga me da k'udirin da mahaifiyarta ta saka a gaba Wanda ba ya jin hakan mai bulle masu ne su dukan su. **** ***** Challa na tsaye farfar ta shige gida sannan ya juya ga fadarsu. Duk inda ya wuce sai an sunkuya cike da girmamawa har ya isa. Kai tsaye ya shiga falon mahaifiyarshi, idan ta na da uzuri yasan ba zai sameta a falon ba ta na can cikin ƙuryar ɗakin ta. A yanzun ma bai ganta ba sai ya samu wuri ya zauna kafin ta ji alamun zuwanshi ta fito. Ta na zaune ta lanƙwashe ƙafafuwa hannuwanta biyu duk a saman cinyoyin ta ta jirkitasu ta sama, kan ta a duƙu. Gefe da gefenta hayaƙi na tashi a hankali ya na karaɗe ɗakin. Kusan awwnni biyu kenan da zamanta wurin. Ta buɗe idanunta a hankali da sukai kore shar ta ɗaura a kan mijinta da ke ɗan nesa kaɗan da ita, na wani lokaci kafin ta ƙara rufe idon. "Da kyau Amba!" ya faɗi da murmushi kwance a fuskarshi. Ita ma ta mai da mashi martanin murmushi sannan ta miƙe. "Ɗana ya zo ya na jira na" ya gyaɗa mata kai ta fice da ga ɗakin. Inda ta adana mashi abincin shi ta nufa ta fara ɗakko mashi ta aje a gaban shi sannan ita ma ta zauna. Ya taso ta shafa kanshi sanna ya koma ya zauna. Ta buɗe gasashshen nama da kayan marmari ta tura a gabanshi. Duk da ta san ya ci abinci, asalima ita ke haɗa mashi abincin ya tafi da shi duk idan zai tafi bakin ruwa, hakan ba zai hana ya na dawowa ta umarce shi da cin wani ba. A kwai soyayya sosai a tsakanin ɗa da uwar. ****** ********
  • ummee auwal eemran
  • Bilkisu Adam
Previous
Next
© 2021 Bakandamiya  -  About Us  -  Terms  -  Privacy  -  Advertise  -  Support  -  Stock Photos  -  Contact Us  -  Mobile Apps
  • Facebook
  • Twitter
  • Linkedin
  • Youtube
  • Pinterest
  • Instagram
Create New Content
  • Kasuwa
Add Link