• Contrast
    • Font
    • A
  • Sign In
  • Sign Up
    Loading ...
View All Updates Mark All Read
Bakandamiya
  • Shafin Farko
  • Mambobi
  • Zauruka
    • Browse Groups
  • Tambayoyi
  • Ra'ayoyi
    • Browse Polls
  • Makalu
    • Browse Entries
  • Bidiyoyi
    • Browse Videos
  • Sautuka
    • Nemo Sautuka
  • Hotuna
    • Browse Albums
    • Browse Photos
  • More
    • Kasuwa
      • Stores Home
      • Browse Stores
      • Browse Locations
      • Products Home
      • Browse Products
      • Products Pinboard
      • Categories
      • Browse Reviews
      • Wishlists
    • Sana'o'i
      • Browse Listings
    • Sanarwa
      • Bukukuwa Masu Zuwa
      • Past Events
  • Updates
  • About
  • Abokai(4)

Updates

About

Personal Information

  • Suna Muwaffaq
  • Sunan Mahaifi Salis Nabage
  • Jinsi Na miji
  • Ranar Haihuwa July 17, 1998
  • Takaitaccen Bayani Suna na muwaffaq dan shakera 22 dalibi a jami'ar taraya dake karshe ne mutum ne mai son karance karance

Contact Address

  • Sunan Gari Jos
  • Karamar Hukuma Jos ta arewa
  • Jaha Kano
  • Kasa Nigeria

Abokai

  • Jibrin Adamu Rano ZOBENA 02 ©Jibrin Adamu Rano Bayan ta sa ƙaninta ya ɗakko mana tabarma ta shimfina mana a rumfar ƙofar gidan su mun zauna ne na fara bata labarin BABI NA FARKO    "A wata makaranta ce ta 'ya'yan masu yatsu da yawa al'amarin ya faru, yau kimanin shekaru shida zuwa bakwai da bamu labarin..."    "Su waye kuma masu yatsu da yawa?" Nafisa ta tari numfashina.    "Masu hannu da shuni mana." Na yi maganar cikin yanayi na murmushi da mamakin yadda aka yi ta kasa ganewa. Abin da ya ƙara bani mamaki shi ne shima hannu mai shunin bata san me ake nufi da shi ba, don haka ne na yi mata ta yaren gwari.    "Masu kuɗi nake nufi to." Na ɗan tsahirta kana na ci gaba.    "Makaranta ce sakandire ta mata zalla, makaranta ce ta jeki ki dawo. Amma fa kamar yadda na faɗa miki duk yarinyar da kika gani a cikin wannan makarantar ko dai 'yar mai kuɗi ce ko kuma wani ne ya tsaya mata.    To a ajin manyan ɗalibai na makarantar ne wasu ɗalibai su biyu Salima da Rufaida suna zaune suna rubutu kamar da wasa Rufaida ta ƙyalla ido a kan yatsan Salima wanda ta hangi wani zobe na gwal mai matukar ƙyalli a jiki. Cikin wani yanayi na murna, ɗoki da kuma zumuɗin ganin zoben ta fara yiwa ƙawar tata magana.    " 'Yar rainin wayo! Dama ke kika ɗaukar min zobena kina ji ina ta cikiya kika yimin kunnen uwar shegu? To asirin ki ya tonu na gan shi sai ki bani abuna." Ta yi maganar ne cikin dariya, don haka Salima ta yi tunanin cewa zoben ne ya burgeta shi ya sa take tsokanarta. Kawai sai itama ta yi dariya bacin ta fakaici idon malamin da yake yi musu darasi a wannan lokacin kar ya hangosu suna surutu, ta yi magana cikin raɗa-raɗa.    "Kema zoben ya yi miki kyau kenan?" Bata jira ta amsa ba ta ci gaba.    "Wallahi Muttaƙa ne ya bani shi jiya da daddare da ya zo gidanmu zance, kowa dai yana yabawa da zoben." Jin haka ne ya sa Rufaida haɗe rai, tunaninta ta yaya Salima za ta raina mata hankali, ta sace mata zoben da saurayinta Kamal ya bata tana cewa itama wai saurayinta Muttaƙa ne ya bata. Don haka rai a ɓace ta sake jaddada ƙudirinta cewa lallai nata ne.    "Don Allah ba na son wasa ki bani zobena tunda dai na riga na gan shi. Wallahi zoben nan da kike gani tun daga Indiya Kamal ya kawo min, shi ya sa kika ga na damu sosai da ɓatan shi saboda nasan halin Kamal cewa zai yi ban damu da shi ba ne shi ya sa har na yi sakaci da zoben shi ya ɓata." Ta ƙarasa maganar ta na mai miƙa hannunta kan yatsan na Salima da niyyar ta cire zobenta kamar yadda zuciyarta take raya mata ta yi.      "Mtwsss..!" Salima ta ja tsaki ganin yadda Rufaida ta wani daƙumi zoben zata fusge mata shi.    " Bana son iskanci. Don Allah sakar min zobena ni kar ki sa ya yi datti, don Wallahi ina ji da Zoben nan kamar yadda nake ji da Muttaƙana, shi kuwa Muttaƙana ina ji da shi kamar yadda na ke ji da raina. Kinga kuwa bai kamata ki yi min irin wannan wasan ba don gudun kar a samu matsala." Ta ƙarasa da dariya dai dai lokacin da ta fusge hannunta daga cikin na ƙawar tata tana mai bin zoben da kallo tare da yabawa da yadda yake ta faman wani sheƙi da walwali.    Rufaida fuska a ɗaure ta ce    "Wasa!" Ta maimaita kalmar ne tana kallonta da alamun mamaki.    "Ban gane me kike nufi da wasa ba? Ko an faɗa miki yadda ba kya wasa da abin da ya shafi Muttaƙa nima ina yin wasa da duk abin da ya shafi Kamal ne? Don Allah ni ki cire min zobena ki bani bana son iskanci da wulaƙanci." Ta ƙare tana turɓune fuska, a wannan karon yanayinta ya fi koyaushe nuna cewa lallai da gaske take furucin zoben nata ne.    Abin na ƙawayen biyu kamar da wasa haka ya fara, kafin daga bisani da kowaccen su ta fahimci ashe fa da gaske ƙawar tata take yi. Ita Rufaida kallon ɓarauniya take yiwa Salima wacce ta sace mata zobenta da ta daɗe tana nema, zobenta da ɓatan shi har bacci ya hanata yi. Yayin da ita kuma Salima take kallo Rufaida a matsayin wata hamshaƙiyar 'yar rainin hankali wacce tana ji tana gani Muttaƙanta ya bata zobe amma zata dinga da'awar wai nata ne har tana daƙumar mata shi. Wannan shi ne abin da ya sa rigima ta kacamewa ƙawayen biyu a cikin ajin ta yadda dole sai da Malamin ya fahimta, rigimar da ta yi ƙarfin da ta fi ƙarfin malamin har ta je gaban shugabar makarantar Hajiya Rukuba Maryama (Kamar yadda take amfani da sunan). Hajiya Maryam cikin takaici da ɓacin rai take tambayarsu abin da ya haɗa su har suke faɗa a gaban malam, sanadin da ya sa malamin mai amsa suna malam Nasir ya ɗakko zoben kenan yake nunawa shugabar makarantar akan abin da suke faɗan. Hajiya Maryama ta karɓi kyakkyawan zoben da ya burgeta bisa ganin yadda yake ta faman wani sheƙi da walwali tana jujjuya shi a hannunta cikin ƙare masa kallo da tunanin lallai zoben kam ya cancanta a yi rigima a kan shi saboda kyan tsarin shi da alamar da ke nuna tsadar shi. Aikuwa kafin ta bud'i baki ta yi magana yarinyarta budurwa sa'ar matasan 'yan-matan biyu Salima da Rufaida mai amsa suna Hajara da take zaune a kan kujerar gaban teburinta ta yi farat ta miƙe tsaye tare da bararo idanuwanta waje cikin ƙarewa zoben kallo tare da alamun da ke nuna mamakinta ƙarara ta ce. "Wallahi Umma zobena ne ba nasu ba ne! Wallahi Umma zobena ne wanda nake ta faɗa miki cewa ya ɓata ɗinnan tun kwanaki." Ta furta hakan jikinta har wani rawa-rawa yake yi tana ƙoƙarin fusge zoben a hannun mahaifiyarta. Ba mahaifiyar tata da ta bita da kallo ba, hatta aminan biyu Salima da Rufaida da kuma shi kansa malam Nasir da kallo kawai suka bita kowa zuciyar shi a cunkushe da mamakin yadda daga ganin sarkin fawa zaisa har miyarta ta yi zaƙi haka, daga ganin zobe kawai sai ta ce zobenta ne?"
  • Ameera Garba Rabbana ateena fiddunya hasanatan wafeel akheerati hasanatan waqna azabannarrr! 👏👏👏
  • Fatima  sheriff 
  • Ibrahim Musa Gamba INDA RABBANA BA WAHALA...!!!
Previous
Next
© 2021 Bakandamiya  -  About Us  -  Terms  -  Privacy  -  Advertise  -  Support  -  Stock Photos  -  Contact Us  -  Mobile Apps
  • Facebook
  • Twitter
  • Linkedin
  • Youtube
  • Pinterest
  • Instagram
Create New Content
  • Kasuwa
Add Link