• Contrast
    • Font
    • A
  • Sign In
  • Sign Up
    Loading ...
View All Updates Mark All Read
Bakandamiya
  • Shafin Farko
  • Mambobi
  • Zauruka
    • Browse Groups
  • Tambayoyi
  • Ra'ayoyi
    • Browse Polls
  • Makalu
    • Browse Entries
  • Bidiyoyi
    • Browse Videos
  • Sautuka
    • Nemo Sautuka
  • Hotuna
    • Browse Albums
    • Browse Photos
  • More
    • Kasuwa
      • Stores Home
      • Browse Stores
      • Browse Locations
      • Products Home
      • Browse Products
      • Products Pinboard
      • Categories
      • Browse Reviews
      • Wishlists
    • Sana'o'i
      • Browse Listings
    • Sanarwa
      • Bukukuwa Masu Zuwa
      • Past Events
  • Updates
  • About
  • Abokai(20)

Updates

About

Personal Information

  • Suna Zannah Mustapha
  • Sunan Mahaifi Wakil
  • Jinsi Na miji
  • Ranar Haihuwa January 4, 1992
  • Takaitaccen Bayani Wanne irin bayani ?

Contact Address

  • Sunan Gari Geidam Hausari behind police station
  • Karamar Hukuma Geidam
  • Jaha Yobe
  • Kasa Nigeria

Abokai

  • Rahmatu Lawan LESSON 1: SUBJECT-VERB AGREEMENT Subject-verb agreement, also known as CONCORD, is the relationship that exists between a subject and a verb in English. In other words, your subject must agree with your verb in all grammatical relationships, such as the person, the number etc. Concord is one of the tricky areas of learning English, especially for second language learners – people who had already learned another language before learning English. We see people with over 20 years of experience, learning and using the English language, but still having a slip of the tongue or genuinely making mistakes when it comes to stitching their subjects with their verbs in English. Perhaps the best way to remedy the difficulties of mastering concord is to regularly practice. Another way could be to get hold of its knowledge and get our head around the skills. Whichever way you are most comfortable with, practice is not an option; it is a must! To learn about the subject-verb agreement in English it is important to understand the concepts of SUBJECT and VERB. What do we mean when we say subject or verb in English? Another thing we should also know is the ENGLISH TENSE, that is, the different time frames through which our actions are expressed; in other words, do we speak about the past, the present or the future? One can say there are three tenses in English: the present, the past and the future. But each of these three is further classified into more categories, for example, present simple, present continuous, present perfect and so on. I will take each one of these to explain with examples and try my best to show you how subject-verb agreement is fused in all of them, and how best a learner can absorb the knowledge and demonstrate the skills. SUBJECT and VERB We will continue on SUBJECT and VERB in the next lesson in shaa Allah. EXERCISE Now, with the little explanation so far, let’s see in YOUR OWN WORDS, what do you understand by the concept CONCORD or SUBJECT-VERB AGREEMENT? Write your answer in the comment section below. Daga zauren @English Q & A
  • Lawan Dalha Ya Allah Ka sada mu da alkhairan da ke cikin wannan rana; ka tsare mu daga sharri duniya da lahira. #JummaaMubarak
  • Ayusher Muhd JALILAH - Babi Na 3 https://youtu.be/qSwjodj1neo
  • Maryamerh Abdul Wasa-wasa, karatun boko na neman fin karfin talaka a najeriya. Allah mun tuba
  • Aisha Sa'eed Abubakar (Aishan Umma) *AHALINA* *Na* *Aishan Umma* *???????? ZAMAN AMANA WRITER'S (Z.A.W)* https://www.facebook.com/ZAMAN-AMANA-Writers-FANS-311893699485963/ 2019 1 Cike da zumud'in yau zasu zauna da mahaifansu ababen alfaharinsu suka tashi daga bacci, sakamakon yau babu makaranta. A gaggauce Fahat yayi wanka yasa Aida ma taje tayi sannan yayiwa sauran k'annensa guda biyu, duk suka shirya sannan suka fito. Fahat ne yayi saurin shiga kitchen dan anan ya jiyo motsin Amminsu, har k'asa ya tsuguna ya gaisheta, suma sauran k'annensa da suka shigo kitchen d'in yadda suka ga d'an uwansu yayi hakan sukayi, ta amsa cike da fara'a had'i da kulawa, duk seda ta shafa kawunansu tana mai karanta musu addu'ar da Annabi Sallalahu alaihi wa sallam yake karantawa Hassan da Hussaini (u'izukuma bi kalimatillahi tammat min kulli shaid'anin wa hamma, wa min kullu ainin lamma). Tana matuk'ar son yaranta, sosai take k'aunarsu, har wani lokacin takanyi tunanin Kodai mutuwa zatayi ta barsu ne?. Fahat ne ya katse mata tunaninta ta hanyar cewa "Ammi bari naje na gaida Abbu na dawo na tayaki da wani abin mana se mufi yin sauri". "A'a d'an albarka jeka ku gaisa d'in daga nan kuje ku gyara d'akunanku tukunna ni na k'arasa wannan" cewar Ammi Kafewa yayi yace "ai tunda babu school yau to zan tayaki aiki insha Allah, Habibtyna ina k'aunarki, bana son naga kina gajiya da yawa. Mene amfanin Allah ya baki ni amma na gagara taimaka miki, gaskiya inde kina so na samu lada ki bari na tayaki kinji Ammi na?" Tayi murmushi had'e da shafa kanshi tace "na amince to yaron kirki, kaida kake namiji kaine me son shiga kitchen ita kam Aida ko a jikinta, yanzu ko nace tazo muyinma se raina ya kusan b'aci, ban san inda ta koyi k'uiya ba. Allah ya raya mana ku, ya tsareku ya kare ku, Allah yayi muku albarka ya kareku dukkan sharri, ina alfahari da samunku masoya na sanyin idaniyata." Daga haka ya je ya gaida mahaifinsu, se gashi ya dawo tare da Aida suka ci gaba da aikinsu suna hirarsu ta tsakanin uwa da yaranta. A haka ta dad'a samu tayi ta yi musu nasiha akan halin rayuwa. Su ko su Sa'eed da Alim suna can wajen mahaifinnasu suna tayashi hira sakamakon weekend baya zuwa ko ina. A haka suma suka kammala aikinsu suka fito da komai suka jere a dinning area, kowa kuma ya hallara akayi bismillah aka fara cin abinci cikin ladabi. Haka rayuwar gidan take tafiya cikin aminci gashi dai ba wani me kud'i bane me gidan sedai rufin asirin Allah da kuma wadatar zuci, amma zuciyar mutanen gidan tana cike da k'aunar juna da kuma tausayawa. Iyayen suna k'ok'arin ganin sun bawa yaransu tarbiyya daidai gwargwardo, haka ma yaran suna biyayya ga iyayen nasu, duk kuwa da irin soyayyar da suke nuna musu hakan besa raini ya shiga tsakaninsu ba. Rayuwar gidan abar sha'awa ce ga duk wanda ya gani sedai san barka. Alhaji Nasir Aliyu (Abbu) shine mahaifinsu Fahat, se mahaifiyarsu Maryam, sunyi aure tsawon shekara goma sha bakwai kenan a yanzu. Allah ya azurtasu da yara hud'u Fahat shine babba wanda yake da shekara goma sha shida, se Aida take bi masa ita kuma tana da shekara goma sha d'aya, se Sa'eed me shekara bakwai, sannan auta Alim me shekara hud'u a duniya. A yanzu haka Fahat yana SS 2 a makaranta sannan yayi saukar Al Qur'an tun yana shekara sha hud'u yanzu hadda yake, ita kuma Aida tana Pri. 6 itama takai kusan izifi 30 a Al Qur'an, Sa'eed yana Pri. 2 yana uzifi 10 a Al Qur'an, se auta Alim yana Nur. 2 shi kuma izifi biyu a Al Qur'an Kwatsam wata ranar Juma'a bayan su Fahat sun tafi makaranta wani irin ciwon ciki ya taso Ammi a gaba, da k'yar ta iya lalubar wayarta ta kira Abbu ta sanar masa, cikin tashin hankali shima ya baro office domin yaga meke damunta har haka?, dan tabbas duk ciwon da Maryam zata bud'e baki ta fad'a harta kira a waya ba k'aramin ciwo bane. Da hanzari ya shiga d'akin ganin halin da take cikine ya sashi fita nemo mota dan baze iya d'aukarta a babur ba cikin wannan halin. Allah sarki Ammi! Allah ya baki lafiya ???? *Aishan Umma* ??????????????
  • Umar Yakubu liman Ynb
  • Fadima Fayau He who loves the world injuries his hereafter
  • Rabee'atou A Oumar (Pinky) 🌖 *BAMBANCIN HALITTA* 🌖 ©️℘ıŋƙყ wattpad😛inkylady222 Email😲umarrabiatu@gmail.com 02 *Kyanko* *2001* ƙaton fili ne da ya ke cike maƙil da jama'a, a na ta hayaniya a na maida yadda akai. tsawon lokaci kafin wasu murguza murguzan mutane da babu komai a jikinsu sai 'dan fantare da su ke a k'ugunsu, su ka buɗe ƙatuwar muryar da Allah yai masu su ka fara kwarara ihu da ke shaidawa jama'ar wurin Ambarama ta iso. A take kowanne yaja bakinshi ya rufe suka sunkuya cike da girmamawa har ta ƙaraso ta zauna a kujerar da ta ke ta ƙaton dutse ce aka lanƙwasa sannan akai mata ado. Wurin ya ɗau wani kalar shirun da ko allurar ka ta faɗi zaka iya jin sautin faɗuwarta. Bayan yan daƙiƙu da zaman ta waɗannan margaza-margazan mutanen su ka iso filin jaye da wani tsoho da ke ɗaure da kaca ya na tafiya daƙyar jikin shi duk ya farfashe. A ka Duƙar dashi gaban Ambarama ya sadda kanshi ƙasa Ɗaya da ga cikin mutanen Ambarama ya fara jawabi. "Kamar yadda kuwa ya sani game da zunibin da Ayuroro ya aikata a nahiyar nan da sauran nahiyoyi maƙwabtanmu, wanda sanadiyyar hakan ta jawo ɓarna da sanadiyyar rayuka aruaru ta kuma jaza tarzomar da ba a daɗe da kwantar da ita ba." "..a yanzu bayan shekaru ukku kamar yadda shari'a da doka ta tsara tare kuma da taimakon sarauniya mai girma Abin kwatance Ambarama ta tanada, hukun cin Ayuroro na farko zai hau kan shi." "Lafiya, tsayon rai Ambarw" "lafiya mai girma Ambara" jama'ar wurin ke faɗi cikin amanna da duk wani hukuncin ta. Mutanen ta suka ɗaga hannu akai shiru. Ɗaya da ga jikin su ya taho da wani ƙoƙo ya aje gaban ayuroro. "Dakata!" Ambarama ta faɗi akaron farko ta na kallon Ayuroro da ke niyyar ɗaukar ƙoƙon. Ya tsaya jikin shi na ɓari hawayen shi duk sun bushe. A yanzu bai da sauran hawayen da zasu kuma zubowa kuma, ya riga da yasan abin da zai faru a ƙarshe kenan. Ahalin shi sun zama cutuwa a gareshi, sun jefashi cikin bala'en da bai isa ya fidda kan shi ba. "Ka koma a salin halittarta kafin ɗaukar hukunci." Maganar ta ta katse tunanin shi. Ta na rufe baki ya haɗe hannuwanshi wuri ɗaya tare da girgiza sai ga ƙaton maciji sharɓeɓe ya bayyana. An riga an gama duk wani bayanin da za ai, kowa yasan hukuncin abin da ya aikata. Ya sulala ya kafa kanshi a ƙoƙon ya ruza halshenshi ya surɓe abin da ke ciki. Dandanan ya fara yamutsewa ya na komawa ɗan ƙarami kamar sabon macijin da aka haifa. A cikin jinga jingan nan wasu suka taho da wani abu mai saƙa-saƙa mai shara-sharar da ana hangen abin da ke ciki tamkar gilas, suka aje gaban macijin sannan suka ɗauke shi su ka saka a ciki suka maida marfin suka rufe. Ambarama ta kalli abun wani abu kamar walƙiya ya fito da ga bakin ta ya bugi abun ƙara ta karaɗe wurin har ana toshe kunnuwa. Daga nan sai ta bada umar nin a ɗauke abun ta tashi. Kowa ya watse, wasu fuskarsu da alhini. ***** ****** ***** Ambara na komawa gida ta shige ɗakin ta tare da sallamar masu hidimta mata ta buga ƙara, ihu da kukan baƙin ciki. Ta saka ranta da bayyanar duk gaskiyar da ta ke son sani ga lamarin nan ko dan ta san yadda zata bullowa lamarin ta haɗa iyalanta. A matsayinta na shugaba a yanzu amma ace ba ta da kowa nata bata da jinin da zata kalla ta ji daɗi. Kuka ta ke mai cin rai, kukan kaɗaici. Ta ɗauki lokaci mai tsawo ta na wannan kukan kafin ta gaji ta bari sannan ta bada dokar ba zata ga kowa ba har tsawon kwana bakwai. *Mafarin komai* *1999* Zaune ta ke bisa ƙaton dutse ta zura ƙafafuwanta cikin makeken ruwan da ke wucewa, ta kuma zuba mashi idanuwa a zahiri. A kai-akai ta ke jefa ƙananun duwatsun da ke dumtse a hannunta cikin ruwan. Kusan Sati biyu kenan amma ta kasa mantawa da maganar mahaifiyarta 'maima' _idon ki ya rufe da ganin gaskiyar kalamaina 'Farfar', kin makance da soyayyar da ba zata amfane ki ba._ _ya zama dole kuma ki goyi bayana na mulki *kyanko!*_ ta saka hannu ta gyara gashin kanta da iska ke kaɗowa a fuskarta. Ta sunkuya ta sake dumtso duwatsun saboda ƙarewar da na hannunta sukai. Tunani ta ke son yi, mafita ta ke so. Amma ta yaya? wanda ya ke bata dukkan mafita a yawan lokutta,yanzu matsalar da ga nan ta fito. Jikinta ya bata kallonta ake, dutsen da ta ware za ta jefa ta fasa. "Idan ka ci gaba da tsayuwa a nan, kwarjininka zai iya saka tunani na gushewa" ya tako a hankali cikin tafiyarshi ta cikakkun maza masu jini a jika. Ya saka hannunshi ya tattare gashinta ya maida shi gefen wuyanta. Sannan ya leƙo da kan shi ta ɗayan ɓarin har ta na shakar numfashin shi ya ce "A mabiya kyanko ne kawai challa ke da kwarjini. A wurin ki kuma tamkar jaririn da ki ka haifa ne" ta lumshe idanuwanta ta buɗesu a hankali. Sannan ta kamo hannunshi ya zagayo ya zauna gefen ta. "Sai ki ka zo ke ɗaya, ki ka baro ni ko. mai ya sa?" Ya faɗi sa'ilin da ya sauke jikkar da ke rataye a wuyanshi. "Ha ka kawai yau na riga ka zuwa kafin cikar lokaci" "To shikenan in dai ba laifi na yi ba da sauƙi" ya ɗebo duwatsun ya fara jefawa. Ta kalli yawan ruwan yadda suke tafiya har ba a iya ganin ƙarshe su. Ta ce "Challa" "uhm?" ya amsa ya na kallonta. "Ni ina son na tsallake ruwan nan ina son shiga.." Sai ta ɗan yi shiru ta na tunani "Ya sunan nahiyar?" "Mwagbo" ya bata amsa ya na murmushi. "Yauwa mwagbo.. ina son ganin yadda su ke rayuwarsu. Wai ba irin ta mu ba? addininsu daban?" ya gyaɗa mata kai. "ina son shiga" "kar ki damu babu in da ba zaki zagaya ba ma idan lokaci ya yi _Boidi_ (princess)" Sai ta yi murmushi ta ce "wa ne kalar addini suke?" "kayya dai! Ba ni da ikon gaya maki akan hakan Boidi a yanzu" Ta tsuke fuskarta ta mik'e ta na had'e rai, maganar maima na dawo mata. ' _ke fa ba za ki ta b'a samun cikakken 'yancin da za ki ziyarci dukkan inda kike so ba Matuk'ar mulkin kyanko ba naki ba ne_ ' Ta cije leb'en ta na k'asa ta na jin haushin challa, mo ba komai ai an riga an masu baiko, zuwa yanzu ya ka mata ace tasan duk wani abu da ta ke son sani gane da ko wace nahiya. Ya ruk'o hannunta. Ta juya mashi ba ya ta na k'in kallin shi. "haba Boidin challa, bai kyautu mu samu sab'ani a kan abin da kin riga kin sani ba. Babu wanda ya ke da damar tsallake nahiyarmu ko jin halin da wata nahiya ta ke ciki nusamman mwagbo, sai jinin mulkin kyanko. Ke kuma duka mai ya rage? Da ga munyi aurenmu kin haihu shikenan fa zaki san koma miye. Ki bar damuwar nan kin ji?" Ta gyad'a kai. "yauwa yimun murmushin nan in gani" Ta murmusa ba dan ta so ba. Ta na son challa sosai a gefe d'aya kuma ta fara kwad'ayin abin da mahaifiyarta ke kwad'aita mata gaje kyanko gaba d'aya. Ya jawo jikkar da ya zo da ita ya d'akko k'aton ganyen da ya nad'o gasasshen nama a ciki. K'amshin naman ya bugi hancinta, yawunta ya tsinke ya zarce mak'ogoron ta. Idan akwai abin da ta fi so gasasshen nama ne. Kasancewar a gaba d'aya nayihar babu mai ikon cin naman da aka dafa sai masu mulkin nahiyar, duk kuwa da naman shine abincin su kawai a ko yaushe, hakan kuma bai dame su ba tun da haka tsarin yake haka kowa ya tashi ya ga a nayi. Idan kana da wani had'i da su ko wani a ciki ya baka za ka iya ci amman kai ba ka da damar gasa nama. "mu ci abincin nan kar yai sanyi" Ta matsa kusa da shi ta zauna su ka fara Cin abincin, su na yi yana mata fira har suka gama. Sai da duhu ya fara sannan su ka bar wurin har gida ya raka ta inda ko ina zagaye ya ke da duwatse da su ake zagaye ko ina afidda gida je a cijin gidan ma dasu ake fidda d'akuna. A gaba gudansu sun dad'e suna fira kafin yai nata sallama ya tafi. "ni dai ban ga amfanin soyayyar nan ba farfar" Tai dariya ta zauna kusa da ita. "mama kenan, kin san challa ya na so na sosai Ni ma kuma ina son shi. Bayan nan ana darajamu da girmama mu mama gashi zan shiga gidan shugaba amatsayin suruka, challa zai zama shugaba.." "ke ni rufe mani baki" Ta katse ta. "kibar ganin kamar zaki samu duk ikon da kike tunani. Eh zaki samu sosai amma ba komai ba, idan ki na ganin abin da na ke gaya maki k'arya ne ki jira ki auri challan. Ina nai rantse maki da mahaifinki sai kin yi nadamar k'in bani had'in kai da ki kai" Farfar tai shiru ta na juya maganar mahaifiyarta a ranta. Ita ma maima ba ta ce mata komai ba ta barta tai tunanin da zai fisshesu su duka. Tunanin yai mata yawa ta kasa karkata ga b'angare d'aya sai kawai ta tashi ta shige d'akin da babanta ke had'a magungunan shi. Ya na zaune ya juya baya ya na duba wasu shafukan takardu rubutun ciki mai haske. Ya na dubawa ya na had'a magungunan shi. Tsaye ta yi har ya gama ya rufe maganin acikin k'atuwar kwalba sannan ya juyo ya fuskance ta. "a rayuwa ba komai kake so kake samu ba duk kuwa ga yadda ka so abunnan. Hakuri da yadda tsarin rayuwa ya zo maka shi zai sa ka tayu cikin farinciki da kwanciyar hankali" Ta sadda kanta k'asa ta na murmushi Ta ce "to baba, nagode k'warai" Ya jinjina kai, sanna ya ciga ba da yi mata nasiha mai hannun ka mai sanda ga me da k'udirin da mahaifiyarta ta saka a gaba Wanda ba ya jin hakan mai bulle masu ne su dukan su. **** ***** Challa na tsaye farfar ta shige gida sannan ya juya ga fadarsu. Duk inda ya wuce sai an sunkuya cike da girmamawa har ya isa. Kai tsaye ya shiga falon mahaifiyarshi, idan ta na da uzuri yasan ba zai sameta a falon ba ta na can cikin ƙuryar ɗakin ta. A yanzun ma bai ganta ba sai ya samu wuri ya zauna kafin ta ji alamun zuwanshi ta fito. Ta na zaune ta lanƙwashe ƙafafuwa hannuwanta biyu duk a saman cinyoyin ta ta jirkitasu ta sama, kan ta a duƙu. Gefe da gefenta hayaƙi na tashi a hankali ya na karaɗe ɗakin. Kusan awwnni biyu kenan da zamanta wurin. Ta buɗe idanunta a hankali da sukai kore shar ta ɗaura a kan mijinta da ke ɗan nesa kaɗan da ita, na wani lokaci kafin ta ƙara rufe idon. "Da kyau Amba!" ya faɗi da murmushi kwance a fuskarshi. Ita ma ta mai da mashi martanin murmushi sannan ta miƙe. "Ɗana ya zo ya na jira na" ya gyaɗa mata kai ta fice da ga ɗakin. Inda ta adana mashi abincin shi ta nufa ta fara ɗakko mashi ta aje a gaban shi sannan ita ma ta zauna. Ya taso ta shafa kanshi sanna ya koma ya zauna. Ta buɗe gasashshen nama da kayan marmari ta tura a gabanshi. Duk da ta san ya ci abinci, asalima ita ke haɗa mashi abincin ya tafi da shi duk idan zai tafi bakin ruwa, hakan ba zai hana ya na dawowa ta umarce shi da cin wani ba. A kwai soyayya sosai a tsakanin ɗa da uwar. ****** ********
  • saadiyya husaini 1.114 2.Abu hassan Abu malili Al shadhili ya rasa a 939 A.H a cairo. 3.sayyaduna usman sbd ya aure yayan manzon Allah guda biyu rukayya da ummu khursim 4.Na r ibn muhammad abu al laythal-samardaqandi 5 bazara-zara 6.shamuwa-uwa 7.Niger (niger state) 8.1october 1960
  • Ameera Garba Qur'ani 2:155 وَلَنَبۡلُوَنَّكُم بِشَىۡءٍ مِّنَ ٱلۡخَوۡفِ وَٱلۡجُوعِ وَنَقۡصٍ مِّنَ ٱلۡأَمۡوَٰلِ وَٱلۡأَنفُسِ وَٱلثَّمَرَٰتِۗ وَبَشِّرِ ٱلصَّٰبِرِينَ And We will surely test you with something of fear and hunger and a loss of wealth and lives and fruits, but give good tidings to the patient.
Previous
Next
© 2021 Bakandamiya  -  About Us  -  Terms  -  Privacy  -  Advertise  -  Support Center  -  Mobile Apps  -  Contact Us
  • Facebook
  • Twitter
  • Linkedin
  • Youtube
  • Pinterest
  • Instagram