Create Account

You will use your email address to login.

Password must be at least 6 characters and contain one upper and one lower case letter, one number and one special character. The password should not contain special characters \ , / & : .

Enter your password again for confirmation.

This will be the end of your profile link, for example:
http://bakandamiya.com/profile/yourname

 
 

Member Sign In

If you already have an account, please enter your details below. If you don't have one yet, please sign up first.

 
 
 
Forgot Password?
Bakandamiya
All
  • Everywhere
  • Forums
  • Blog Entries
  • Classifieds
  • Videos
  • Album Photos
  • Shafin Farko
  • Mambobi
  • Tambayoyi
  • Zauruka
  • Sanarwa
  • Ra'ayoyi
  • Makalu
  • Bidiyoyi
  • Sautuka
  • Hotuna
  • Sana'o'i

Login

 
 
 
Forgot Password?
Sign Up

Sign Up

Create Account

You will use your email address to login.

Password must be at least 6 characters and contain one upper and one lower case letter, one number and one special character. The password should not contain special characters \ , / & : .

Enter your password again for confirmation.

This will be the end of your profile link, for example:
http://bakandamiya.com/profile/yourname

 
 
Login
  • Sign In
  • Sign Up
All
  • Everywhere
  • Forums
  • Blog Entries
  • Classifieds
  • Videos
  • Album Photos
  • Shafin Farko
  • Mambobi
  • Tambayoyi
  • Zauruka
  • Sanarwa
  • Ra'ayoyi
  • Makalu
  • Bidiyoyi
  • Sautuka
  • Hotuna
  • Sana'o'i
  • Updates
  • About
  • Abokai(13)
  • Makalu(1)
  • Hotuna

Updates

Loading
  • qurratulayn salees
  • Everyone
Loading Loading ...
  • Zuhrah Abdulhamid Hassan
    Zuhrah Abdulhamid Hassan is now friends with qurratulayn salees.
    Nov 30
    • Translate
  • Hameedah Abubakar
    Hameedah Abubakar is now friends with qurratulayn salees.
    Nov 6
    • Translate
  • Sabi'u Ya'u Gama
    Sabi'u Ya'u Gama is now friends with qurratulayn salees.
    Oct 31
    • Translate
  • qurratulayn salees
    qurratulayn salees commented on Kingboy's blog entry.
    Oct 31
    Masha Allah
    MUTUWA NAKE SO
    MUTUWA NAKE SO
    MUTUWA NAKE SO
    Labarin 'yar madigo

    KINGBOY...  more
    MUTUWA NAKE SO
    Labarin 'yar madigo

    KINGBOY ISAH

    Tsaye take bakin babban titi wanda motoci da ba-bura ke ta faman
    wucewa mutane kowa na uzurin gabansa. Budurwa ce yar shekara 25
    hannunta rike da leda irin ta masu yoyon fitsari. Fuskarta duk ta
    lalace al...  
    • Translate
    • 5 person reacted on this
    • qurratulayn salees
      qurratulayn salees Masha Allah
      • Oct 31
  • qurratulayn salees
    qurratulayn salees liked Yasinu Sani Umar's photo.
    Oct 31
    • 4 person reacted on this
  • Kamala Minna
    Kamala Minna is now friends with qurratulayn salees.
    Oct 30
    • Translate
  • qurratulayn salees
    qurratulayn salees is now friends with Bamai Dabuwa .
    Oct 30
    • Translate
  •  Kingboy
    Kingboy is now friends with qurratulayn salees.
    Oct 29
    • Translate
  • Rufaida  Umar
    Rufaida Umar is now friends with qurratulayn salees.
    Oct 28
    • Translate
  • Almu Dakata
    Almu Dakata is now friends with qurratulayn salees.
    Oct 28
    • Translate
  • Rahma Kabir
    Rahma Kabir is now friends with qurratulayn salees.
    Oct 26
    • Translate
  • qurratulayn salees
    qurratulayn salees posted a new blog:
    Oct 26
    JINI BAYA MAGANIN ƘISHIRWA
    JINI BAYA MAGANIN ƘISHIRWA
     *JINI BAYA MAGANIN ƘISHIRWA.*    

    Na
    QURRATUL-AYN.

    NAGARTA WRITERS...  more
     *JINI BAYA MAGANIN ƘISHIRWA.*    

    Na
    QURRATUL-AYN.

    NAGARTA WRITERS ASSOCIATIONS.

    BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
                   

                   01

     ...  
    • 7 person reacted on this
    • qurratulayn salees
      Iliyasu Ahmed koda ta masoyi
      • Oct 28
    • qurratulayn salees
      qurratulayn salees yes
      • Oct 30
    • qurratulayn salees
      Bamai Dabuwa Da kyau
      • Oct 30
    • qurratulayn salees
      Kamala Minna sannu da kokari
      • Oct 31
    • qurratulayn salees
      Kingboy Da kyau
      • Oct 31
  • Zahra A. Alkali
    Zahra A. Alkali is now friends with qurratulayn salees.
    Oct 26
    • Translate
  • Nasiru Yunusa
    Nasiru Yunusa is now friends with qurratulayn salees.
    Oct 26
    • Translate
  • qurratulayn salees
    qurratulayn salees has just signed up. Say hello!
    Oct 24
    • Bakandamiya and Kamala Minna reacted on this.
    • qurratulayn salees
      Kingboy ????
      • Oct 25
View More
Loading Loading ...
There are no more results to show.

About

Personal Information

  • Suna qurratulayn
  • Sunan Mahaifi salees
  • Jinsi Mace
  • Relationship Status Single
  • Ranar Haihuwa April 25, 2019
  • Kasa Nigeria

Contact Information

  • Sunan Gari kano
  • Karamar Hukuma Dala
  • Jaha kano

Personal Details

  • Takaitaccen Bayani Haifaffiyar kasar Nigeriya, zaunanniyar Kano, ina rayuwa a karamar hukumar dala ta jahar Kano.

Abokai

  • Bakandamiya Hello
  • Zuhrah Abdulhamid Hassan
  • Nasiru Yunusa
  • Kingboy
  • Sabi'u Ya'u Gama
  • Rahma Kabir
  • Bamai Dabuwa
  • Kamala Minna NAƘASAR ZUCCI!. Kamala Minna (gajeran labari) "Ki tafi gidanku na sake ki!" Runtse idanu na yi jin sautin muryar Adamu a kaina, yana furta kalaman da suka kusan sanya ni haihuwar cikin da ke jikina. Da sauri na dago jajayen idanuwana da suka gajiya da kuka na sauke a saitin sa. Wani irin tashin hankali da ciwon rai suka  dirar mani, ji nake kamar na daura hannu a kai na kurma ihu ko zan samu raguwar tashin hankalin da nake ciki, amma ina, ba na tunanin hakan zai yi wani tasiri ko na yi, domin kuwa ba shi da amfani. Runtse idanuwa na yi ina jin yadda kalaman Adamu ke sake ihu a kaina, ban san me zan ce ba, ban san ya zan fahimci kalubalen da nake ciki a yanzu ba. Na jima da sanin akwai rana irin wannan da za ta fado rayuwata, na san ba ni da mafita a cikinta, domin kuwa komai ya faru tunanina yana ba ni ni ce sila, in da ban yarda na auri Adamu ba, ba yadda za a yi a irin wannan lokacin na dare wanda kowanne bawa yana kwance yana huta wa ransa, amma ni kuma ina nan ina amsar takardar sakina daga hannun mijina. Me ya fi wannan torzarci a rayuwata, a matsayina na 'ya mace? Ji na yi ana tunkuɗa ni gami da kokarin tada ni daga inda nake zaune. Da sauri na kwato kaina daga duniyar tunanin da na afka, Adamu ne a kaina idanuwansa sun kaɗa sunyi jajir kamar wanda aka ɗiga wa dakakken barkono sai faman hirji yake yi kamar zai ci babu. "Tashi ki tafi gidanku Badi'a, na yafe zama da ke a matsayin matar aure gare ni". Ya sake fadi. Yana tura ni waje gami da banko kofar dakin da karfi. Durkushewa na yi kasa, wanda hakan ya yi sanadiyyar bugar cikin da ke jikina, wani irin zafi da zugi ne suka ziyarce ni, da sauri na runtse idanuna ina jin yadda duniyar ke sauya mani, ji nake yi kamar tashin alkiyamata ce ta zo. Sosai nake jin sanyi a jiki saboda lokacin na sanyi ne gashi ko mayafi babu a jikina da zai taimaka min wajen kare kaina. Ban damu ba don na san tashin hankalin da nake ciki ya shallake komai a yanzu. Wai ni ce aka watso waje kamar wata kayan wanki. Wai ni ce aka tsana aka kore ni cikin dare, kodayake ba zan yi mamaki  ba, in na yi duba da sanadin da ya kawo haka. "Na tsane ki Badi'a na tsani auranki! Ki je na yafe miki zama da ni, na yafe wallahi ki tafi gidan ku". Sautin Muryar Adamu kenan da nake jiyowa daga cikin daki cikin wani irin yanayi mai kama da kuka. Hakan ya kara rikitar min da guntuwar natsuwa ta da na yi zaton ta yi saura a gare ni. Wai ni ce yau Adamu ya tsana. Wai ni ce yau ya kora. Kaicon wannan rana! Na sani rayuwata ta gama lalacewa, ba ta da wani amfani. Miƙewa na yi cikin matsanancin yanayi ga zafin da nake ji a duk lokacin da na ji cikin na juyawa, wanda na tabbata ya bugu ne a sa'ilin da na durkushe. Shima kenan da bai zo duniya ba, ya fara sanin tashin hankalin da ke cikinta, ina ga kuma ya zo, ai lamarin ba zai kallu ba. Zuciyata na ji ta tsinke, ina tunanin makomar abin da ke cikina, wanda na tabbata in har na haife shi kashin mutum sai ya fishi kyan gani ga idanun mutane. 'Ina kika dosa?'. Na ji wani sashi na zuciyata ya sanar da ni hakan. Sosai na ji duniyar ta sake hautsine mani, ba abin da nake tunawa sai maganar mahaifina a ranar da aka daura mani aure na zama matar Adamu. "In har kika yi sake wani abu ya fallasa akan lamarin nan, kar ki sake ki tunkaro mani gida, ki nemi wani wajan da za ki kafa rayuwarki". Abin da  mahaifina kenan ya sanar da ni wanda na tabbata har kasan zuciyarsa  haka ne, ba abin da ba zai aikata ba in na yi duba da yadda ya dauki son rai ya fifita shi ga komai, sannan ya dauki kunyar duniya ya fifita akan kunyar lahirarsa. Runtse idanu na yi zuciyata na sake narkewa da tashin hankali matsananci, ban san ina zan dosa ba, ban san wacce alkibla zan fuskanta ba. Na san ba ni da damar daukar kafafuwana na doshi gidan mu don na san kallon arziki ba zan samu ba. Juyawa na yi na dubi dakina na aure. A da kafin Adamu ya gille igiyoyin auren namu wan da bai haura wata daya da kwanaki ba, amma a yau na zama bazawara wacce aka sake ta tsakar dare. A hankali na shiga taka kafafuwa na na doshi kofar da za ta fidda ni daga gidan Adamu a matsayin sakakkiya, zan fita ne ba tare da na san inda na dosa ba, na sani na gama rayuwa a filin duniya tunda aure na ya mutu, abin da nake tutiya da shi wanda ya fi komai a rayuwata wanda shi ne zai rufamin asiri, tun da ya balle ai rayuwar tawa ce gabadaya ta balle. Tafiya nake yi cikin duhun daren bayan na fice daga cikin gidan Adamu. Garin ya yi tsit ba ka jin motsi sai kukan g'yare da karnuka, gabana ya shiga yankewa yana faduwa wai ni ce yau nake bin dare na ballo daga gidan mijina ina tafiya, tafiyar da ban san ina za ta kai ni ba, ba ni da gurin zuwa, na sani ba ni da damar tunkarar gidan mahaifina don na tabbata ba zan samu karbuwa ba ko ta dakika daya daga gare shi, mahaifiyata ce mai jin tausayina, ita kadai ce wacce za ta ji k'aina ita ce mai share mani kuka na, ita ce kawai take kalubalantar yanayin da nake ciki. Ina tsoron zuwa gare ta, don na san in har na je zan iya jawo mata matsala ita ma a gidan auren ta, igiyoyinta za su iya ballewa kamar yadda nawa suka balle. Ba zan so haka ba, ba zan so a ce ta dalilina mahaifiyata ta rasa gidan aurenta ba. 'can ya kamata ki nufa, domin kuwa ba ki da wani wajan zuwa illa gidan mahaifanki'. Wani sashi na zuciyata na ji ya bijiro mani da wannan tunanin. Shiru na yi kamar mai son canko wani abu, na ji wani kwarin guiwa ya zo mani akan na tafi gidan iyayena, can ne ya fi dacewa da ni. Hakan kuwa aka yi. Ina isa kofar gidanmu da yake ba nisa da gidan tsohon mijina Adamu, gidan a kargame, na same shi kamar yadda na yi zato. Zuciyata ba ta karye ba, sai kara min kwarin guiwa take. A hankali na shiga kwakwasawa, gabana na daɗa tsinkewa. "Waye a nan?". Na ji sautin muryar mahaifiyata. Hakan ba karamin mamaki ya ba ni ba, jin ita ta amsa a maimakon na ji ta mahaifina wanda nake jira ya bude yana gani na yayi mani korar kare. "Ni ce!" Na amsa ta cikin rawar murya. Shiru ne ya gitta tsakani. Na sani, cewa Mahaifiyata ta gane ni, na sani fargaba da mamaki suka cika ta shi ya sa ba ta sake tanka mani  ba. Na san tunanin mafarki za ta kawo wa lamarin nawa ba wai a zahirance ba. "Badi'a!" Na ji ta ambata tana kokarin buɗe kofar. Ban amsa ta ba, illa wasu hawaye masu ɗumi da na ji sun wanke mani fuska, tausayinta nake ji, tausayi mai tsanani. Na san mahaifiyata ta fi kowa shiga tashin hankali da halin da nake ciki, ita kaɗai ce a duniyar nan wacce ta kula ni, ta karɓe ni da ƙaddarar da na samu kaina, in ka zare mahaifina da ƙaninsa Kawu Dantani, wanda shi ya zama kanwa uwar gami wajen sanya mahaifina ya tsane ni, har ya ji ba ya ƙaunar gani na a filin duniyar nan, a dalilin sa na ɓoye sirrin da ke ɓoye. "Ya sake ki ko?". Abin da mahaifiyata ta tare ni da shi ke nan. Bayan ta buɗe ƙofar ta janyo ni zuwa soron gidan. Wani kuka ne na ji ya zo mani ban san lokacin da na sanya hannu na rufe bakina ba, ina girgiza kai. Haske tocilan da ke hannun mahaifiyata shi ne ya ba ni damar ganin yanayin da take ciki, na tsayin wata da kwanaki da na yi ba tare da ita ba. Ta rame, ga suffar shiga damuwa nan duk ta bayyana a gare ta. "Dama na san za a yi haka. Duk lamarin da ba a ɗora shi a turba ta gaskiya ba, ƙarshensa ƙarkon kifi zai yi". Ta sake faɗi tana girgiza kai, ga wasu ƙwalla da suka tarun mata a idanu, duk da ƙoƙarin ɓoyewar da take yi hakan bai hana ni gani ba. "Na shiga uku!" "Badi'a ba ke ce kika shiga uku ba, ni ce na shiga uku, domin dama ke nake jira tuntuni, kuma dama na san kina tafe, shi ya sa tun da kika bar gidan nan ban runtsa ba dare da rana ina zaman jiran ki, don na san wannan auren naki  ba inda zai je, zai ɓalle!". Zare jikina na yi da sauri jin takun tafiya daga tsakar gidanmu, na tabbata mahaifina ne. Da sauri na dubi mahaifiyata, cikin yanayi na firgici idanuna a warwaje, bakina sai karkarwa yake yi. A hankali na shiga ja da baya, ina ƙoƙarin ficewa amma riƙon da na ji mahaifiyata ta yi mani ya katse mani hanzarina. Da idanu na shiga yi mata alamu da ta sake ni, ina tsoron zuwan mahaifin nawa, domin na tabbata ba ni ce zan fi shiga matsala ba, rayuwar auren mahaifiyata nake tsoron faɗawar sa matsala. "Ba in da za ki je Badi'a, nan ne ya fi dacewa da ke, domin kuwa ba ki da inda ya fi nan gidan." Wasu hawaye suka sake kawo mani hari, da sauri na shiga faɗin. "A'a Umma, ki rabu da ni na tafi, ba na son abin da zai kawo saɓani tsakaninki da mahaifina. Ina ƙaunar kwanciyar hankalinki, ba na buƙatar rayuwar aurenki ta yi ƙarƙon kifi. Don Allah ki bar ni na tafi". "Badi'a na bar ki ki tafi fa kika ce? ina za ki tafi in na barki? Shin kina da wani waje wanda ya fi gidan mahaifinki ne? Ko ina za ki shiga a faɗin duniyar nan babu kamar nan ɗin da kike ƙoƙarin guje mawa. Duk matsala duk runtsi da wani ƙalubale da za ki samu a rayuwarki ba inda ya fi gidan mahaifinki, don haka tun wuri ki canza wannan bahagon tunanin naki. Badi'a ba yadda za a yi na bar ki ki tafi. Ke fa 'ya mace ce. Shin ba kya tunanin halin rayuwar zamanin nan da muke ciki? Kina tunanin in kika wuce kika tafi akwai wata daraja da kima da za ki tadda a can din da kike tunanin tafiya...?". "Karima!". Na ji sautin muryar mahaifina kamar dirar aradu. Ban san lokacin da na fizge hannuna ina ƙoƙarin kwasawa da gudu ba. Cikin hanzari mahaifiyata ta taro ni. "Ki bar ta tafi tun kafin na iso wajen nan karima, in kuma ba haka ba wallahi tallahi har ke a yau ɗin nan cikin wannan daren sai kin bar gidan nan". Kalaman da mahaifina ya shiga furtawa ke nan, yana dosowa gare mu, kamar wani mayunwacin zakin da ya hango nama. Gabana ya sake tsinkewa, wani kuka ya ƙwace mani sai ƙoƙarin fizge hannuna nake yi amma ina, na kasa. "Malam ba yadda za a yi ka ce na sake ta ta fice, so kake yi rayuwar da ka bada kamasho akai ta sake ficewa ta kafa mai lasisi ko me? ina ƙaunar 'yata, ina buƙatar rayuwarta ta inganta, ba yadda za ayi ka yankar mata tikitin fara rayuwa wacce ƙarshenta ta yi ƙarkon kifi. Ban shirya fuskantar wannan baƙar ranar ba, wancan ma da aka yi ta ishe ni". Wani kallo na ga mahaifin nawa na watso mana, idanuwansa kamar za su faɗo ƙasa, sai faman hirji yake yi. Ina tsoronsa da kuma abin da zai ɓata masa rai a duniyar nan, domin bai iya ɓacin rai ba, sam-sam ba shi da juriya, don kuwa na ga hakan, wanda sanadin shi ne rayuwar tawa ta koma a baibai. Ma'aikacin reka ne mahaifina a matsayin maigadi sama da shekaru masu dama yake aiki, rana ɗaya ya zo mana da batun an kore shi daga  aiki. Ranar mun shiga tashin hankali ni da mahaifiyata, domin kuwa wannan aikin da shi muka dogara. Cinmu, shanmu, sutturarmu, kudin makarantana, duk wannan aikin ne amma rana daya baƙin labari ya tadda mu, dole muka shiga jaje. Sai dai abin da ba mu sani ba, ashe sanadin korar aikin shi ne kama  mahaifina aka yi dumu-dumu wajen satar kayan gidan reka, ana fidda su ba tare da kowa ya sani ba. Shi ne mai bin dare yana buɗewa, wasu daga cikin ma'aikatan marassa tsoron Allah suna satar kayan shi kuma ana ba shi ɗan hasafi wanda bai taka kara ya karya ba. A rayuwar mahaifina mutum ne mai son abin duniya, bai san babu ba, domin duk ranar da ya kasance ba shi da kudi to a wannan ranar cikin fushi zai wuni da neman rigima da mahaifiyata, sai dai ba ta biye masa ko kaɗan yakan gama faɗace-faɗacensa ya ƙyale ta. Cikin wannan yanayin na rashin aikin yi ƙalubalen rayuwa ya fara dirar mani, domin kuwa makarantar da nake yi mahaifina  zare ni daga cikinta ya yi, ya tabbatar mani ba shi da damar ci gaba da biya mani kudin makaranta. Hakan ya ƙara dagula mani lissafi. Ba yadda na iya, haka na tattara littattafaina da kayan makaranta na cusa a ma'ajiyar da sai baba ta gani, domin na tabbata in ba  wani ikon Allah ba, duk da buri da fata da naci akan karatuna ni da makaranta har abada! Ai kuwa hakan ce ta kasance, mahaifiyata ba yadda ba ta yi da shi a kan nuna masa illar rashin karatuna ba, amma ya yi burus da ita, sai ma cewa da ya yi in tana da kudi ta ci gaba da biya mani, ai ni ma 'yarta ce, ba shi kaɗai ba ne nake da  haƙƙi a kansa, ai tare suka taru suka haife ni. Wannan magana ta yi wa mahaifiyata ciwo sosai da sosai, ba ta ce da shi ƙala ba. Daga wannan rana mahaifiyata ta ɗauri aniyar neman sana'ar yi, kuɗinta na adashe da take yi wanda bai taka kara ya karye ba, shi ta nemi alfarmar a ba ta kwasa ta kurkusa. Da wannan damar ta yi amfani ta fara dafa mani shinkafa garau-garau ina kaiwa bakin titi. Shi kuwa mahaifina ban san abin da ya shiga kansa ba, domin kuwa miƙe ƙafa ya yi ya koma matar gida, ita kuwa mahaifiyata ta zama mijin, komai ya koma gare ta; ci da sha duk ita take yi a 'yar wannan sana'ar. Ba a je ko ina ba muka cinye jarin, shi kuwa mahaifina ko a jikinsa illa masifa da fadace-fadace da ya zaman masa abin yi. A kullu yaumin ba cas ba as. "Amma Malam kana ganin wannan zaman da kake yi shi ne mafita a gare mu? iyali fa gare ka. Ya kamata ka zama jajirtacce a gidanka, rashin aikin reka din nan ba shi ya zama karshen rayuwarka ba. Kyau dai ka yi wani kokarin domin neman abin yi". Mahaifiyata ce ta tari mahaifina da wannan maganar, ganin rayuwar sai kara shurawa take amma ba wani abin da ya canza. Maimakon ya amshi wannan shawara da ta zo masa da ita ta kirki, amma saboda kin Allah ya baɗe idanuwansa da toka ya dube ta. "Ba dole fa! in za ki iya zama da ni a haka ki zauna. In kuma ba za ki iya ba kina iya tafiya, gaba na da nisa baya ce ta tafi". "Haba Malam...!" Da sauri ya daga mata hannu cikin ɗacin rai da nuna fushi a kan maganar da ta yi masa. "Ke Karima! Ni fa ba wani aiki da zan sake nema, tun da an kore ni a wannan shi ke nan. Dama shi kadai ne abin da na dogara da shi, shi kadai ne na iya. Kin ga ke nan a yanzu haka ba ni da wani tasiri. Girma ya zo mani, ba ni da wani waje da zan je na durkusa na nema aikin yi". Ba Ummata kadai ba, hatta ni sai da na firgita da jin kalamansa. Na shiga duban shi. A girme dai ban ga wasu shekaru da mahaifina ke da su ba wanda za su hana shi aiki, ko da kuwa dako ne ba. Yana da lafiyarsa, yana da karfinsa. Ba abin da ya yi rauni daga gareshi, amma yake fadin ba zai iya wani aiki ba. Mahaifiyata ba ta sake bi ta kansa ba tun ranar da ya fadi mata wannan kalaman, haka ta shuri takalmanta ta doshi wajen yan uwanta ba tare da ya san abin da ta je yi ba. Sun taimaka mata da abin da ba a rasa ba, ta dawo ta sake kafa wata sana'ar, muka ci gaba da yin garau-garau ina kaiwa bakin titi kamar yadda na yi a can baya. Sai dai wannan komawa tawa da na yi a karo na biyu ta bambanta da ta farko, domin kuwa na tadda dan'uwan mahaifina kawu Dantani wanda suke 'ya'yan kishiyoyi. Mutum ne shi mai shegen son abin duniya, ga neman matan tsiya, shi ya sa ya kafa kes a nan bakin titi yana sayar da kayan hatsi. Sai dai ya kafa ne da biyu. Na gano hakan ne bayan mun dau lokaci da shi ina zuwa wajen da garau-garau duk macen da ta zo wucewa sai ya kalle ta, ko siyayya kika zo to sai ya tare ki da maganganu, wanda suka kamata da wanda ba su kamata ba. Ba ya kunyar ya saki baki ya fadi maganganu marassa dadi a gabana, a matsayina na 'yarsa. Ban taba zaton wani abu mai kama da haka zai faru tsakanina da shi ba. Ya fara ja na da wasa kamar dai gaske. Na yi mamakin haka da farko don ban taba zaton akwai rana daidai da daya ba zai zo mani da sakakkiyar fuska ba. A rayuwar da na yi da sanin sa bai taba duba na da idanun kirki ba, iyaka ta da shi gaisuwa in ya ga dama ya amsa, in bai ga dama ba sai dai ya hantare ni. Abu kamar wasa muka saba da shi, har ta kai ta kawo yana kara mani kudi a ciniki, ko in wani irin yan tasha din nan ya ci ya hana ni kudi sai ya biya ni. A cikin haka muka hadu da Adamu, ya nuna yana so na, domin mutum ne mai mutunci da sanin ya kamata, ba ruwansa. Duk da lokacin shekaruna ba su haura sha shidda ba haka muka kulla soyayya da Adamu sai dai a lokacin kawu Dantani sam bai kaunar haka, domin kullum cikin kawo mani ƙauli da ba'adi yake, wajen kushe Adamu. Duk hakan bai sa na ji na canza daga matsayin da na bai wa Adamu a zuciyata ba. "Badi'a zo na aike ki wajen Suwaiba". Kamar daga sama na ji sautin Muryar Kawun nawa daga cikin dan kes din nasa. Da hanzari na mike ban kawo  komai ba na isa gare shi. Leda ya miko mani dauke da kayan cefane. "Kai wa Suwaiba, ki ce mata ina nan zuwa". Gyaɗa masa kai na yi. Haka kawai na ji gabana na faɗuwa, musamman irin kallon da na ga yana yi mani wanda ban taɓa ganin hakan ba. Shi dai ba kallon fushi ba ne balle na ce fushi yake yi da ni. Kallo ne wanda na kasa fassara irin shi. Da wannan tunani na kwashi ƙafafuwana na tafi, zuciyata cike da saƙe-saƙe, har na isa. Sai dai abin mamaki ban tadda kowa a gidan ba, dakin Suwaiba a kulle. Hakan da na gani ya tabbatar mani ba ta nan shiru na yi ina wani tunani. Shin in zauna na jira ta ne ko kuwa na maida masa kayan? Wata zuciya ta ce da ni 'zauna ki jira ta, kila ba nisa ta yi ba.' Haka na samu waje na zauna jikina sukuku ba alamun ƙarfi kamar wata maras lafiya. Sosai na faɗa tunanin rayuwa. Ban yi zato ba kawai na ji alamun motsi a kaina, na buɗe idanuna na ga kawu Ɗantani kaina sai faman bi na yake yi da kallo kamar zai haɗiye ni, yana faman lasar laɓɓansa. "Suwaiba ba ta nan don haka yau ke ce za ki maye gurbinta. Na daɗe ina jin wani iri a game da ke, yau kuma nake so ki amince da ni Badi'a, ba tare da kowa ya sani ba muyi mu gama ba wanda ya sani". Wata irin faɗuwar gaba na ji ta ziryarce ni. Ban san lokacin da na miƙe jikina ya shiga karkarwa ba, a hankali na shiga ja da baya. Wani tashin hankali na ji ya kara ziyarta ta. Ban san lokacin da na fashe da kuka ba lokacin da na gama fuskantar inda ya dosa da batun sa, ina ja da baya a hankali, ban yi aune ba kawai na ji ya cafke ni gami da rufe mani baki. Nan na shiga kiciniyar ƙwatar kaina amma ina, kafin na yi wani yunƙuri na ji ya tura mani wani abu cikin hanci. Kafin lokaci kaɗan na fice daga hayyacina. Daga wannan lokacin ban sake sanin in da kaina yake ba, sai dai na farka na gan ni yashe tsakar gida, mahaifiyata ta ɗora hannu aka, sai faman kuka take, idanuwanta sun ƙaɗa sun yi jajur. Gabaɗaya ta gama ficewa daga hayyacinta. Daga wannan lokacin kwanyata da zuciyata suka fara tariyo mani abin da  ya faru. Ban san lokacin da na fashe da kuka ba. Na zabura ina kokarin tashi amma ina, na kasa. Wani irin zafi da zugi  nake ji a tsakanin cinyoyina. Ji nake yi kamar ana caccaka min kibiya a tsakanina. Ban san lokacin da na sulale zuwa kasa ba. "Badi'a waye ya aikata miki wannan mugun abun? Waye ya shirya ganin rayuwarki ta yi ƙarkon kifi? Badi'a faɗa min waye sanadin aikin nan? Ki faɗa mani!". Wani ƙunci na ji ya ziyarce ni, ba wanda nake tunawa sai Kawu Ɗantani. Zuciyata na ji ta yi kumburi kamar za ta faso waje. Wai ƙanin mahaifina shi ne ya yi mani wannan aikin. Wannan wacce irin rayuwa ce? Wannan wacce irin baƙar rana ce a gareni?. "Meye abin kuka a nan? Ai duk abin da ya faru ke ce sila. Tun da ke ce sanadin da aka ba ta min ƴa. Ke ce sanadin komai". Muryar mahaifina kenan na ji yana faɗin haka cikin halin ko in kula da nuna halin da nake ciki. "Malam ko dai ni ce na fi kowa rashin imani a filin duniyar nan, ba yadda za ayi na so ƴar cikina rayuwarta ta ɓaci. Kuma ka sani komai ya faru da ƴar nan kai ne sila". Wannan shi ne sanadin komai da ya faru a rayuwata Ƙanin mahaifina ya ɓata min rayuwa sannan ya zama silar da ya sanya mai sona ya guje mani, domin kuwa Adamu bai san da ciki ya aure ni ba sai da na kwanta rashin lafiya a gidansa ya kai ni asibiti aka tabbatar masa da cewa juna biyu gare ni har na tsawon wata uku, bayan an yi rufa-rufa an aura masa ni wanda mahaifina shi ne ya zama silar komai har ya yi ikirarin in har wani a cikinmu ni da mahaifiyata muka fasa abin da ke ɓoye sai dai mu san inda dare ya yi mana... "ku fice ku bar mani gida". Muryar mahaifina ta katse mani dogon tunanin da na afka. "Ba in da za mu wallahi. Domin kuwa nan gidan shi ne mazauninmu in ka kore ni ƴarka dole ka bar ta a gidan, kuma wannan abin da ya faru da Badi'a kai ne sanadin komai." Cikin muryar kuka da jin furucin da ke wanzuwa tsakanin iyayena ya ƙara tsinkar mani da zuciya. Da sauri na durƙushe na dubi mahaifiyata. "Umma don girman Allah ki sake ni na tafi. Komai zai faru da ni na yarda amma ba na bukatar a ce komai nawa ya shafe ki. Na yarda zan bar gidansa, zan tafi tunda ba ya son gani na, amma...". Dukan da na ji a bakina ne ya sanya ni saurin tsagaita abin da nake faɗi na sake rushewa da kuka. "Badi'a in har na cika mahaifiyarki ban so na sake jin kin yi yinkurin barin gidan mahaifinki, domin ba ki da inda ya fi shi. Ni na ji zan bar gidan domin dama can ɗauko ni aka yi aka kawo ni ba a nan aka halicce ni ba". Wani tunani ya faɗo mani. Lokaci guda na miƙe abin da nake ɓoyewa wanda shi ne silar komai shi zan faɗi ba zan manta ba, kafin aurena da Adamu sosai Kawuna ya yi ikrarin kashe ni, in har na furta wanda ya yi mani wannan aika-aikar. Lokacin kurarinsa ya yi tasiri a kaina, har hakan ya hana ni faɗa wa Umma wanda ya yi mani wannan aikin. Ba yadda ba ta yi da ni ba, na ce mata ban sani ba. Duban su na yi dukkan su har da mahaifina da yake ta faman hirji. "Kawu Ɗantani!" Shiru ya gitta tsakaninmu. Lokaci guda na ga Umma ta shiga duba na, cikin rashin fahimta kafin na ɗora da faɗin. "Shi ne sila Umma. shi ne ya yi mani wannan aikin ba wani ba ne...". Tun kafin na dire kalamaina, mahaifina ya yanke jiki ya faɗi, tamkar matacce. Ummata kuwa mutuwar tsaye ta yi na ɗan lokaci, kafin ta dawo hayyacinta. Ta shiga duba na tana zamewa zuwa kasa, ta yi zaman ƴan bori. Tashin hankali maras musaltuwa ya bayyana a fuskarta. Wannan faɗuwa da mahaifina ya yi  ita ce ta zama silar shanyewar ɓarin jiki gare shi, domin kuwa jininsa ne ya hau a lokaci guda. Umma kuwa hawayenta kasa tsayawa suka yi daga idanuwanta. Haka muka kasance cikin bakin ciki da ɓacin rai abu goma da ashirin, rashin lafiyar mahaifina, cikin da nake ɗauke da shi, ga rashin walwala a duk fuskokinmu. Na rasa wa zan ɗorawa alhakin faruwa hakan, mahaifina da son abun duniya ya kaishi ga goyon bayan mutanen banza ya aikata ba daidai ba. Kokuwa irin naƙasar da zuciyarshi ta samu wajen tattare hannunshi ya zauna ɗaki wai ba zai iya nemo mana abinda zamu ci ba. Ko kuwa ni da na biyewa rashin wayau da ƙuruciyata na rika amsar kuɗin Ɗantani har ta kai ga wannan abun ya faru da ni. Kodai Ɗantani da ta shi naƙasasshiyar zuciyar  ta ja shi ga aikata mun fyaɗe ba tare da ya yi tunanin zumunci, da kuma halin da rayuwata za ta shiga a gaba ba. Dama duk wanda ya saba shinshine - shinshine, to tabbas zai shinshino abun da ya fi ƙarfin hancinshi. Kamar dai yadda Ɗantani ya aikata fyaɗe a kan wata ƙaramar yarinya, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwarta. In da shi kuma aka yanke mashi hukuncin zaman gidan yari na har ƙarshen numfashinshi, tare da tara me tsanani. Karshe!!!
  • Zahra A. Alkali ???? _*????ιĸιмaн ????rιтer'ѕ ????ѕѕocιaтιon*_    ????( _*Kυngιya Daya Taмĸar Dυвυ*_) Hikmahwritersassociation2019@gmail.com                            loadιng...........✍???? ???? *R̥ͦḀͦY̥ͦU̥ͦW̥ͦḀͦR̥ͦ Z̥ͦḀͦM̥ͦḀͦN̥ͦI̥ͦ*   ( _K̥ͦO̥ͦ S̥ͦO̥ͦN̥ͦ Z̥ͦU̥ͦC̥ͦI̥ͦY̥ͦḀͦ_) W̥ͦr̥ͦi̥ͦt̥ͦt̥ͦe̥ͦn̥ͦ b̥ͦy̥ͦ _*Z̥ͦḁͦh̥ͦr̥ͦḁͦ Ḁͦ Ḁͦl̥ͦk̥ͦḁͦl̥ͦi̥ͦ (D̥ͦi̥ͦd̥ͦe̥ͦe̥ͦy̥ͦl̥ͦo̥ͦv̥ͦ)*_ Dedicated to Autan Hikima???? _B̥ͦI̥ͦS̥ͦM̥ͦI̥ͦL̥ͦL̥ͦḀͦH̥ͦI̥ͦR̥ͦ R̥ͦḀͦH̥ͦM̥ͦḀͦN̥ͦI̥ͦR̥ͦ R̥ͦḀͦH̥ͦI̥ͦM̥ͦ_ 3⃣♾4⃣ Raihan na komawa office ya aiki masinga akan yaje yace ma head din ko wani department yana son ganinsa aconference hall, babu 6ata lokaci duk yabi ya fadamusu kafin ya koma ya sanar da zuwansu. Yana zaune a office kafin ya fara komai yaga hoton kannen nasa dake cikin karamin frame fuskar  Muhievert ya shafa yace "I love you sister but you won't understand why am always harsh toward you change for good please (inasonki kanwata amma ba zaki gane mai yasa nake takuraki ba, dan Allah ki chanja hali)" ya fad'a yana murmushi sallaman Baba masinja ne ya katse mishi tunani bayan ya amsa masa sai yace ya duba mishi office din Abbu koya iso bai dade ba ya dawo yace ya iso, tashi yayi ya wuce conference hall bai kai minti goma ba yaji sun shigo tashi yayi ya kira Abbu kafin ya dawo ya zauna ajerin kujerun da ke jikin babban table din babu dadewa Abbu ya fito atare suka tashi sai da ya zauna sannan suka gaisheshi suma suka zauna babu 6ata lokaci kowa ya gabatar da duk ayyukan da akayi acikin Department dinsa da yake duk sun saba da barin record hakan ya saukaka musu k'ar6a Abbu yayi ya fara gani, inda za'ayi signing yayi inda yaga da bukatan karin bayani sai ya sake tambaya kafin Raihan yayi stamping sannan ya k'ara musu albashi daga kan k'ananan maaikatan zuwa manya kafinnan ya sallame su sosai sukayi murna tare da mishi fatan alkairi. Ammi ce a kitchen tana dafa abinci dan duk kudin su bata wasa da damarta wajen yima mai gida girki in dai ba abunda yaran suke sonci ba duk wani girkin Abbu ita takeyi bata sakaci da hurumin mijinta tana aikinta tana ta salatin Manzo (s.a.w). Chan dai tayi shiru tana tunanin yarta kafin tayi ajiyar zuciya sai da ta gama komai ta kwashe na Abbu akularsa wanda yake daban dana yaran gida harma dana bak'i kafin ta kira kande cikin dadin murya ba cikin nuna isa ba tace idan sun gama gyaran cikin gidan su jera abincin a dining na Abbu su kai sama na yaran abari ak'asa sai su saka turaren wuta aduk kusurwan gidan domin ya fitarda kamshin daya shigo daga kitchen sai Ac shima su kunna dan kamshin ya bada abu mai dadi kafin ta wanke hannunta ta nufi sama. Dakin Abbu ta shiga ta k'ara gyarawa tare da sanya turaren wuta sai d'akinta shima ta gyara ta saka turaren wuta ta kunna Ac kafin ta shiga band'aki ta wanke tas ta fesa airfreshner daganan ta shiga wanka tare dayin alwala fitowa ta shiga shafe shafen su humra don lokacin sallah bai karisa ba, kaya ta saka riga da zani mai manyan pattern wanda akayi design din jikin kayan da pattern din bayan tayi simple makeup ta duba agogo taga har lokacin salla yayi da sauri tasa hijab dinta tayi kabbara bayan ta idar ta dad'e tana yiwa iyayenta da yaranta da mijinta addu'a kafin ta tashi daga kan darduman. Tana idarwa taji horn din mota ajiye hijab din tayi ta fita danyi musu sannu da dawowa. ♾♾♾ Yana karasawa ya bar gurin da gudu saboda ya san halin Goggo sarai yanzun nan sai ta daka mai dundu kama baki tayi tana cewa "yau ni dannan zau ce dama ni na mutu, lallai ubanka zai zo yatarar dani wato har ya haifi dan da zai iya fadamin haka da sauri ta kwalawa Ibro kira ta mika mishi waya ungo danno min layin balarabe yi abu da jiki maza-maza karka 6atamin lokaci" ringing daya biyu ya dauka yana cewa "hello Goggo" tace "elon ubanka, eh nace elon ubanka ko kanada magana ne sai kuma ta fashe da kuka, wato d'an nan katuromin hatsabibin yaronnan saboda yazo ya cimin mutunci koh? ya zageni tatas daga ni har zuria ta balarabe kayi kokari da kai da wannan munafukar matar taka". Kukan data k'ara sawa ya d'aga hankalin Malam Balarabe arikice yace "haba Goggo dan Allah kiyi haku..."  bata bari ya karasa ba tace "nace hakurin ubanka wallahi zan tsine maka tunda baka da mutunci" ta fada tana wurga wayan. Goggo! Goggo!! Goggo!!! Da sauri ta fito tana cin goro tana kokarin gyara zaninta "nace lafiya daiko kake min kira haka ubana dan ko ubana ne kawai zai kirani irin haka banza gantalalle mara mutunci" Hararanta yayi kafin yace "ba lafiya ba Goggo taya za'ayi ke kici abinci ki rage sannan wai inci? ai wannan ci bayane kawai cin abincin da kika rage haka kawai nasan ba wai wani wanke hannu kikayi ba kilama kinaci na bakin naki na komawa ciki but you're expecting me to eat this haba ai wannan abincin dabbobi ne kawai zasu iya ci ni kuma kinga mutunne ba dan kuikuyo ba" salati Goggo tayi ta rike baki tana kallonsa har zata d'auko muciya ta bi bayansa sai kuma ta fasa tace "lalle dannan wuyanka yayi kyauri ya isa yanka, wato nikake fadawa haka saboda ka mugun rainani wlh ba laifinka bane laifin uban kane daya aikoka kaci zarafina kuma na gode amma dan uwarka mai zakaci inba wannan din ba sai dai idan zaka dafa danwake inkuma ba haka ba sai dai fa ka kwana da yunwa". Hararanta yayi yace "cin abincin gidanki ko virus ni kinga tafiyata zanje naci indomie da kwai awajen mai shayi koba komai yafi wannan dattin tuwon da kika rage". Haushine ya kama Goggo kawai ta saka kuka tana cewa "oni yau naga yaro jarababbe aiko iyayenka zan sama duk sai naci mutuncin su". ♾♾♾ Awani babban mall suka tsaya koda taga haka ba tace komai ba dan tasan suna da bukatan sayan kaya saboda haka itama ba tace kala ba ta fita suka shiga kantin vibration din wayanta ne yasa ta tsaya ganin mai kiran yasa tayi murmushi. "Hello darling brother my one and onl...." bai bari ta k'arasa ba  azuciye ya amsa da cewa "waye darling din naki kina matsayin kanwata gida daya muke kwana muke tashi but you cant check on me kullun banganinki da safe, da dare kuma kinyi barci shin me kike nufi me kike tunani kina koyawa yan uwanki eh?" Marairaicewa tayi kafin tace "Yaya plx am sowie yaukan zan jira kadawo cox i really missed you dear kayi hakuri zan kiyaye ba zan sake haka ba kaji"  ok kawai yace har zai kashe wayan sai kuma ya sake cewa "kar ki kuskura ki kai 6 awaje baki dawo gida ba" kafin ma ta amsa ya kashe ta6e baki ta ajiye wayan ta shiga ta iske harsun gama jakarta ta fitar ta cire makudan kudi ta mika musu sannan tace "gashi idan ya rage sai ku raba chanjin. Zaune yake a farfajiyar gidansa yana shan iska Hajiya ta shigo rike da tray babba "barka da hutawa baban Raihana" murmushi yayi kafin yace "yawwa barka dai uwar 'ya'yana wani beta kika had'omin tun dazu kamshi ke tashi? Alhaji kenan baka rabo da zolaya. "Ammi me kika dafa mana" Zahra data dawo daga makaranta kenan ta hangosu a gurin shan iska shine ta nufi gurin dan ta gaishesu hannu ta mika zata bude flask din cikin zolaya Hajiya ta buge hannunta tana cewa "ban sani ba yar nema kije dinning naku yana chan "haba Ammi ni gaskya da Abbu zanci koh Abbuna? ya amsa mata da eh yana murmushi. Ammi tace "haba dan Allah wallahi kai kake shagwaba su da yawa saboda meye ba zataje gurin yan uwanta ba?. "Yawwa ai naji dadin haka gwanda data zauna kinga Ammi shikenan sai in had'a da nata da nawa duk saina cinye" Raihan ya fad'a dan neman tsokala. Ammi tace "gaskiya kam gwanda kayi hakan" aiko tanajin haka ta ta6e baki tayi kitchen aguje shima yabi bayanta yana dariya rufe kofan yayi tayi ta ihun ya budeta amma yaki Ammi kam bata kulasu ba ta mijinta takeyi shi kuma Abbu bai kula ba sai da yazo shiga shine ya bude daya ganta yayi dariya kad'an yana bata hakuri dan yasan Zahra akwai daru. "Hello kana inane kazo yanzu? a dayan bangaren Sulaiman yace "yanzu na ajiye su daddy agida "ok na baka nanda mintina talatin karka kuskura ka wuce hakan kasameni a gidan Anty Raihana" tsaki yaji kasa kasa kafin yace "ok toh angama saina zo" tsaki tayi tace "karma kazo nidai na baka minti talatin. Anty Raihana data tsura mata ido tace "kedai baki rabo da masifa toh Allah kyauta miki" dariya tayi tace "amen Anti ni kinsan bana son bata time" Anty Raihana tace "wai kwata kwata minti nawa kika min daza kice nanda minti talatin" dariya tayi sannan tace "ahaba Anty wallahi na kai awa biyu kuma kinsan yau inason inga yan gida musanman yaya Raihan saboda 3wk kenan ban ganshi ba har gwara Zahra muna ganin juna a school su Yazid kam na manta when last muka had'u shiyasa zan koma da wuri Anty tace "lalle ma yarinyannan wai wato kinfi karfin kije gaida Raihan ne kafim ki fita school ko kuma what d reason behind this you ur stupidity? ta6e baki tayi tace "kai dan Allah Anty ni banda tym ne shiyasa. _*D̥ͦI̥ͦD̥ͦE̥ͦE̥ͦY̥ͦL̥ͦO̥ͦV̥ͦ T̥ͦḀͦK̥ͦU̥ͦC̥ͦE̥ͦ*_ lιĸe coммenт ѕнare ????ѕannυ ѕannυ вaтa нana zυwa ѕaι daι adad'e вa'aje вa.✍????
  • Rufaida Umar NADAMAR FURUCI ©Rufaida Umar. "Hoo! Ka ji kunya! Wallahi ka ji kunya! Tirr! Da miji irinka!" Wata siririyar mace ce ta ci ɗamara a daidai majalisar wasu dattawa tana sababi. Wanda ake dominsa, ya sunkuyar da kai yana jin wani raɗaɗi a ƙasan ransa. Ga yara da manya an taru ana kallonsu. Wani tsamurmurin dattijo dake gefensa ya dubi matar yana nuna ta da yatsan shi manuniya. "Wallahi Asabe ki ji tsoron Allah, ki tuba tun kafin lokaci ya ƙure miki! Wane irin wulakanci ne za ki biyo mijinki bainar jama'a ki ci mutuncinsa? Ƙarin aure a kansa aka fara ne?" Jin haka ya sa ta yi kan Dattijon nan da sababi. "Kai Amadu! Wallahi ka yi gaggawar fita daga idanuna na runtse! Dama ai ko ba ka nuna hali ba na san ku ne munafukan da ke hure mishi kunne! Wato ga annoba, yana kawo muku karya da gaskiya a kaina kuna haɗuwa ku zage ni tas! Hakan kaɗai bai yi muku ba sai da kuka ga zai auro min sa'ar ɗiyata. Kai ai da ace ma na samu ciki da wuri da tuni na aurar da Yaha. Amma tsabar wulaƙanci, a rasa wa za a haɗa ni kishi da ita sai yarinya ƴar bana-bakwai! To wallahi karr nake kallo ku! Aure ne dai ina raye Murtala bai isa ya yi shi ba. Idan kuwa yana ja da ni to mu zuba mu gani! Ya dai ji kunya wallahi, an girma ba a san an girma ba!" Ran dattijan ya ɓaci, Sule wanda ya fi su harzuƙa ya miƙe tsaye jiki yana rawa. "Mutuniyar banza da wofi! Yau kin ƙara tabbatar da ko ke wace ce! Na yi tirr da shawarar da na ba Murtala na aurenki, da ace na san za ki zame mishi bala'i da masifa da ban soma ba! Kuma Asabe mutuwa ce sai dai ki yi, aure dai babu fashi! Ɗan'uwanmu ba zai mutu da annoba irinki ba! Shashasha kawai!" Wata irin shewa ta sanya gami da sakin guɗa tana rausaya kai kamar taɓaɓɓiya. "Ayyiriri nanaye! Yaro bai san wuta ba sai ya taka wallahi! Mu zuba mu gani Sule, gobe dai za a daura aure ko? To, ni Asabe na ce mu zuba, na ga uban da ya isa ya ɗaurawa Murtala aure. Zan kashe mutum na kashe banza wallahi! Duk abin da ya biyo baya ka yi kuka da kanka!" Daga haka ta bar wajen tana sababi da kururuwa da cika-baki. Murtala har lokacin bai ɗago ba sai zubar da hawaye, sai da Amadu ya kori dukkan jama'ar da suka taru kafin ya soma yi wa Murtala magana cikin faɗa-faɗa. "Me ya sa ba za ka iya sakin wannan matar ba? Haƙuri na me kake yi da ita har haka Murtala? Cin mutumcin da take maka ya yi yawa kai kuwa kamar ma ba gani kake ba! Akan wane dalili? Idan yara ne Allah Ya raya maka su. Amman wannan cin mutumcin da me ya yi kama?" Sule ya yi ƙwafa. "Ka ƙyale shi! Tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa kan doka ai, na ce ka rabu da shi kawai Amadu! Kunnen Murtala ba ya jin laifin Asabe, idanuwansa ban ce suna gani ba. Amman na rantse da Allah ba macen da ta isa na zauna ta ci mutumcina irin haka! Ka zama namiji, kuka aikin banza ne! Wannan ba matar rufin asiri ba ce." Shi dai Murtala ba baka sai kunne, ya gama sauraronsu, da ƙyar ya saki ransa bayan sun ƙarashe da yi mishi nasiha mai kwantar da zuciya kafin daga bisani su hau zolayarsa akan amaryar da zai yi. Nan ya ɗan sake amman labarin zuciya a tambayi fuska. *** Washegari da misalin ƙarfe takwas, Asabe ce tsaye ƙiƙam a ƙofar ɗakin Murtala tana dakon fitowarsa duk kuwa da ta sanya sakata ta rufe ɗakin gam tun daren jiya da ya dawo gida. Bugun duniya ya yi bata buɗe ba, abinci ma cewa ta yi wanda su Amadu suka ba shi a majalisa ya ishe shi. Da Asuba ma bata buɗe ba shi ma bai ƙwanƙwasa ba. Wannan ya sa tana tashi, ta kasa, ta tsare a bakin ƙofar. Yaranta sai safa da marwa suke yi suna masu jin takaicin halin uwarsu, yayin da masu goya mata baya na yi. Atika wacce ta fi kowannensu tausayin baban nasu ta dube ta. "Haba Umma, don Allah mene ne haka kike yi? Kin hana Baba fita alhalin kin san yau..." "Atika zan ci ubanki! Zan ci ubanki wallahi muddin ba ki fita a hanyata ba. Shegiyar yarinya marar kishin uwa. Ku wuce ku tafi makaranta tun ban karya ƙafafunku ba." Atika ta goge hawayenta, ta ja hannun ƙannenta su biyar suka fice daga gidan. Suna fita ta ci karo da Amadu da Sule sai wani Kawun babansa Murtala a waje. Ta gaishe su. "Kira mana Babanku mana, lokaci na ƙurewa." A sanyaye ta labarta musu abin da ke faruwa. Wannan ya sanya suka shiga gidan da sallama, musamman ma Sule wanda ya fi su shaƙa. Asabe na zaune saman kujera tana girgiza ƙafa tana cin ƙosai mai zafi, ba ta ko jin zafinsa saboda yanda ranta ke suya. Kallon tara saura ta yi musu kafin ta kau da kai tana ƙwafa. "Asabe wace irin mata ce ke? Me ya sa ba kya jin bari?!" Kawu ke wannan maganar cikin tausasan lafazi don a tunaninsa zai sa ta tausaya. Ta miƙe tsaye gami da furzar da ƙosan bakinta, harara ta watsa musu da jajayen idanunta waɗanda kishi ya rinar. "Lamido kake ko Rilwan? To wallahi ba ka isa ka aurar da mijina ga kowace shegiya ba, ba zan yarda ba! Mutu ka raba ni da Murtala! Ba wanda ya isa ya..." Ai bata kai ƙarshe ba, Sule ya dauke ta da kyakkyawan mari yana huci. Wani irin hantsilawa ta yi, ta daka tsalle ta miƙe ta yi kansa tana kantara ashariya. "Ni! Ni za ka mara har gidan aurena Su.." Bata kai ga ƙarasawa ba ya ƙara dauketa da wani marin, ya angiza ta gefe. "An mare ki asararriya! Na ce an mara ɗin! Banza da bata san darajar aure ba! Kuma wallahi kika yi wani yunƙurin hana mu fid da Murtala daga gidan nan sai na zage na ci ubanki!" Ya dubi Amadu. "Amadu buɗe min ƙofar nan!" Amadu ba musu ya ƙarasa ya zare sakata, shi kuwa Sule suna faɗi in faɗa da Asabe wadda ta koma tamkar zararriya. "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" Furucin Amadu ya maido da su hayyacinsu. Gabaɗaya suka dube shi. Kawu ya ƙarasa ɗakin da sauri. Ganin haka duk suka shiga ciki. Abin da suka gani ya yi matuƙar gigita su. Murtala ne kwance, jini na fita ta kunne da hancinsa. Iyakar ruɗewa sun shiga. Wata irin azabbabiyar ƙara Asabe ta saki. Ta juya da zummar fita daga ɗakin sai dai cikin zafin nama Amadu ya tare ƙofar. "Annamimiya! Ina za ki?! Ina za ki je bayan kin kashe shi?!! Babu inda za ki fita!!" Asabe ta fashe da kuka. "Wallahi na rantse da girman Allah ban kashe Murtala ba! Wallahi ban kashe shi ba!" Kawu wanda ke fid da hawaye jikinsa har rawa yake ya dubi Sule. "Sulaimanu, kira ƴansanda." Jin haka gabaɗaya Asabe ta ƙara rikicewa tana haɗa su da Allah su rufa mata asiri, rantsuwa sosai ta shiga yi akan ba ita ta kashe Murtala ba, amman ina! Babu mai sauraronta. Atika na cin karo da gawar Babanta ta fasa ƙara ta faɗi anan ta sume. Hayaniyar ta jawo hankalin makwabta, sai ga shi an soma cika gidan. Babu jimawa Sule ya dawo tare da ƴansanda, Asabe na ta rantsuwar ba ta kashe mijinta ba sai dai babu wanda ya saurareta. Kowa ma ya buɗe baki cewa ya ke yi za ta aikata duba da irin furucin da ta dinga yi na kashe rai. Har tana ikrarin MU ZUBA MU GANI. Da wannan aka tafi da Asabe ofishin 'yansanda. Iyakar binciken ma'aikata ba su gano taƙaimaiman abinda ya kashe Murtala ba. Haka aka ci gaba da tsare Asabe kafin a kammala shari'a. Iyakar gaskiyarta ta faɗa akan ba ta kashe Murtala ba, sai dai babu wanda ya saurareta ballantana ya yarda duba da munanan kalamanta waɗanda da su lauyan dake kare haƙƙin Murtala ya ci galabar da Alƙali ya sa a tsare ta. Kwananta uku a gidan yari, tana zaune zugum tana tunanin munanan halayenta, aka aiko tafiya da ita ta yi baƙo. Bata ta6a zaton akwai wanda zai duba maraicinta ya ziyarce ta ba, haka nan Atika tun a harabar kotu ta ce babu ita ba ita saboda ta kashe ubanta. Bayan an kai ta ɗakin ganawa da baƙi, ta saki baki ganin ba kowa ba ne sai Sule. Wani irin murmushi yake yi mata na mugunta har ta samu wuri ta zauna. Bayan idanu sun ɗauke a kansu ya soma magana. "Asabe kenan, sannu kin ji? Ai dama wanda ya riga ka kwana to zai riga ka tashi. Har kina zaton Ni zan mance irin tsantsar yaudarar da kika yi min a zamanin samartaka? Wannan kaɗan kika gani, sai na sa an kashe ki kamar yanda na ba da Murtala ga Dodon tsafi." Ya dan yi waige-waigensa kafin ya dube ta yana murmushi cikin raɗa ya ce. "Ni ne silar mutuwar mijinki, kuma ni zan zama silar taki mutuwar. Ko a haka na bar ki na kashe ki Asabe! Wannan somin ta6i ne daga ni Sule." Cikin rawar murya ta nuna shi da yatsa. "Kai.. kai...ne..su..?" Dariya ya saki a hankali. "Ƙwarai kuwa, ni ne nan silar mutuwarsa domin a duniya babu abin da nake so ban da shahara da dukiya. Ko ta wane hali sai na samu." Wata razananniyar ƙara ta saki, ta cakume shi da hannayenta tana kuka. "Sule ɗan'uwansa?! Ɗan'uwansa?! Allah Ya isa tsakanina da kai!" Ganin tana neman tona asirinsu ya yi saurin fincikewa, gandiroba ta yi saurin zuwa ta rirriƙeta. Tana zage-zage da tsinuwa sai dai ba wanda ya kula da sambatunta. Sun ga fin haka a gidan yari, Sule na murmushin mugunta har aka shige da ita ciki sannan ya juya ya fice daga wurin zuciyarsa tas ya bar Asabe cikin NADAMAR FURUCI. *KARSHE*
Previous
Next

Makalu

  • JINI BAYA MAGANIN ƘISHIRWA

    Posted Oct 26

     *JINI BAYA MAGANIN ƘISHIRWA.*     Na QURRATUL-AYN. NAGARTA WRITERS ASSOCIATIONS. BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM                                01    Falo ne...

View All Entries

Hotuna

  • Qurratulayn's Photos
  • Albums
View More
© 2019 Bakandamiya Game da Mu Talla Terms Privacy Tuntube mu Android App IOS App
  • Facebook
  • Twitter
  • Linkedin
  • Youtube
  • Pinterest
  • Instagram
Share